Connect with us

Uncategorized

Sojojin Najeriya sun kame wasu yan ta’adda 3, da bindigogi 44

Published

on

at

Advertisement

Rundunar Sojojin Najeriya ta sanar da kama wasu mutane guda uku da ake zargin yan ta’adda ne a jahar yayin da suke safarar bindigu zuwa kauyen Bena dake cikin karamar hukumar Wasagu ta jahar Kebbi, kauyen dake da iyaka da jahar Zamfara.

Advertisement
Advertisement

Kanal Dole ya bayyana sunayen yan ta’addan kamar haka; Aminu Umar dan shekara 32, Shehu Samaila dan shekara 25 da kuma Bilyaminu Abdullahi mai shekaru 22, inda ya kara da cewa sun kama yan ta’addan dauke da bindigu guda arba’in da hudu (44). Haka zalika kaakakin yace sun kwato kwankunan alburusai guda dari uku da hamsin da daya, 351, duk a cikin motar da yan ta’addan suke ciki mai lamban rajista ZUR 28DX Kebbi, yayin da suke kan hanyarsu ta shiga jahar Kebbi. “Bincikenmu ya binciko yan bindigan na kan hanyarsu ta zuwa kauyen Bena ne dake cikin karamar hukumar Wasagu na jahar Kebbi, wanda kuma yana da iyaka da jahar Zamfara. “Wannan kamen da muka yi yazo daya da wani mutumi, Rabiu Akilu da muka kama dauke da bindigogi 36 da alburusai 343 a cikin motarsa yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Zamfara a watan Nuwamba.” Inji shi. Daga karshe kanal Dole yace zasu cigaba da gudanar da bincike akan Aminu, Shehu da Bilyaminu domin jin wanda zasu kai ma makaman da kuma wanda ya basu makaman, don haka yayi kira ga direbobi dasu taimaka ma Sojoji da sahihan bayanai game da ayyukan yan bindiga.

Advertisement

Naija News ta ruwaito Matakan Tsaro sun kama wani mutum mai Suna Musa Mora wanda aka taras da shi da makamai daga garin Babana a Karkarar Borgu ta Jihar Neja.

Advertisement
Advertisement
Advertisement

KarantaAtiku ya sa hannau a takardar yarjejeniyar zaman lafiya ta zaben 2019

Advertisement