Connect with us

Uncategorized

Mutane 14 sun Mutu, 17 da rauni a wata hari a Jihar Kaduna

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Yan Hari sun kai farmaki a garin Ungwan Paa-Gwandara

Wasu yan hari sun kai farmaki da har sun kashe mutane 14, sun kuma yiwa mutane 17 rauni a daren Lahadi da ta gabata, a wata kauye, mai suna Ungwan Paa-Gwandara a yankin Jema’a na Jihar Kaduna.

Mista Joshua Paul, wani mazaunin yankin ya bayyana ga manema labarai a Kafanchan a yau cewa wadanda aka kashe a same su a wata bikin aure daidai karfe takwas (8) na yamma.

“Mutane tara (9) suka rasa rayukan su a lokacin harin, sa annan mutum biyar (5) suka mutu a wannan safiya a Kafanchan General Hospital.

“da sauran wasu sha bakwai (17) hade da yan yara guda shida da suka ji mummunar ciwo da raunuka. har yanzu suna cikin mummunan yanayin,” in ji shi.

Har ila yau, Malama Victoria Martins, da ita ma ta fada ga wannan mugum hari, bayan an kula da ita a asibitin a garin Kafanchan, ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya cewa, Mata da yara ne suka fi samun rauni a wannan harin.

Ciyaman yankin Jema’a, Mr Peter Averik, ya bayyana akan wayar salula da cewa har yanzu bai sami cikakken bayani game da wannan lamarin ba, amma an riga an tsara ‘yan sanda zuwa ga yankin da wannan mugum harin ya faru.

The police was yet to react to the incident at the time of filing this report. However a source said the command would issue a statement later.

Har yanzu ‘yan sanda ba su amsa ga abin da ya faru ba a lokacin bada rahoton nan. Duk da haka wata majiya ta ce za a ba da sanarwa daga nan baya.