Connect with us

Labaran Najeriya

Buhari ya sauya labarin da aka saba yi game da Najeriya – Lalong

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Simon Lalong, Gwamnan Jihar Filato ya ce shugaban kasar Muhammadu Buhari ya sauya labarin da aka saba yi game da Nijeriya a kasashe akan yaki da cin hanci da rashawa.

Lalong ya ce wannan ne a sakon sa na musanman zuwa ga Shugaba Buhari ta hannun Babban shugaba Harkokin Sanarwa, Mista Mark Longyen, a ranar Lahadi a Jos.

“Mai Girma, ka yi nasara wajen canza labarin da aka saba yi game da Najeriya da siffarta a tsakanin  Jam’iyan haɗin gwiwar al’ummomi.

“Buhari ya yi nasarar aiwatar da wanna a sa’ar shi na farko a ofishin,” inji shi.

Lalong, wanda ya taya Shugaba Buhari murna a shirin bukin ranar haihuwar sa ta shekaru 76 wanda zai yi a yau Litini, ya bayyana shi a matsayin mai tsari da kuma tattalin zamantaka na Nijeriya.

Gwamna ya ce, ranar haihuwar Buhari ya tuna masa da cewa ya kasance wani tauraron yaki da cin hanci da rashawa, mai son al’umma duka, mashahuriyar kasa da nagari.

 

Karanta kuma: Za mu gudanar da zaben 2019 tare da dokokin da aka saba da ita – INEC