Connect with us

Uncategorized

Zaben 2019: Mabiya bayan Kwankwaso sun yi Murabus da PDP sun koma APC

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Abubuwa ta cigaba da faruwa kamin zaben 2019

Balaraba Ibrahim Stegert, tsohuwar mataimakiyar Rabiu Kwankwaso ta fita daga Jam’iyyar PDP a ranar Lahadi 16 ga Disamba.

Balaraba har zuwa lokacin da ya yi murabus ya kasance daga magoya bayan Kwankwassiyya.

Yan lokatai a baya, Kwankwaso yayi kira da mabiya bayan sa dan kwantar da hankulan su ta bin gurbin sa ga matakan sa ta barin APC zuwa PDP.

A halin da ake ciki ga siyasar jihar Kano, Balaraba, babban mabiya na Kwankwaso, ya koma APC.

Bayan da aka tsayad da ita a matsayin SA a karkashin shugabancin Abdullahi Umar Ganduje, Balaraba tayi murabus kuma ta komawa babban uba siyasar ta, kakankwaso a jam’iyyar PDP a shekarar 2017.

Janar Idris Bello Danbazzau (rtd), da Hajiya Balaraba Ibrahim sun koma wa jam’iyyar APC bayan da suka yi murabus da jam’iyyar PDP.

Duk da haka, Shugaba Muhammadu Buhari ya kasance dan takarar shugaban kasa mafi rinjayi a shekara ta 2019, kuma kada ‘yan Nijeriya su yadda a yaudare su irin yadda’ yan adawar jam’iyyar PDP ke shirin yi. inji Farfesa Stephen Ocieni.

A fadin Ocieni, wanda yayi jawabi a ralin zaben shugaban kasa a garin Ayingba, Jihar Kogi. Gwamna Yahaya Bello ya kasance mafi kyau ga jihar Kogi kuma har yanzu.

Ministan ya bukaci kada ‘yan Najeriya su bar yan jam’iyyar PDP su yaudare su.

Naija News ta ruwaito PDP sun sha kunya a yayin da Buhari bai Mutu ba a Landan. inji Lai Mohammed.