Connect with us

Uncategorized

PDP: Alkawalin Atiku Abubakar a Jihar Zamfara

Published

on

at

Advertisement

Alhaji Atiku Abubakar, dan takaran shugaban kasa na Jam’iyyar PDP ya gabatar da cewa zai magance halin ta’addanci a kasar, musanman a Jihar Zamfara.

Advertisement
Advertisement

Muna da sani a Naija News Hausa da cewa, Atiku Abubakar da Jam’iyyar PDP sun gudanar da hidimar yakin neman zaben shugaban kasa a Jihar Zamfara, a ranar Litini 4 ga Watan Fabrairu, 2019.

Advertisement

Dan takaran yayi alkawali ga mutanen Zamfara da cewa zai samar da tsaro da kuma magance ta’addanci a Jihar inda an zabe shi a matsayin shugaban kasan Najeriya.

Advertisement
Advertisement

“Idan babu kwanciyar hankali a kasa ko Jiha, ba yadda manoma ko masana’anta zasu ji dadin samar da ayukan su, har ma ayukan addini ba za ta tafi daidai ba” inji Atiku

Advertisement

Jama’ar Zamfara sun yi murna da wannan kuma fitar su ya bayyana wannan.

Advertisement

Kalli yadda mutanen Jihar Zamfara suka fito ga marabtan Atiku:  

Advertisement
Advertisement

Advertisement

Taron mutane na ta tsuwa da kirarin sunar Alhaji Atiku Abubakar (Sai PDP, Sai Wazirin Adamawa).

Advertisement

Atiku ya kara da alkawarin cewa zai gyara, zai kuma tsarafa Mabulbulin ruwa na Bakolori da ke a Jihar Zamfara.

Advertisement
Advertisement

“ko da shike Noma ita ce aikin ainihin aikin mutanen Zamfara, amma ta’addanci da hare-hare daga ‘yan hari da bindiga ya hana mutane zuwa gonakin su, zamu magance wannan da yardan Allah, sa’anan mu baiwa manoma tallafin kayan aikin gona don samar da ayukan su da kyau” inji shi.

Advertisement

Ya karshe da shawartan jama’ar Zamfara da zaben dan takaran Gwamnan Jihar a Jam’iyyar PDP, Bello Matawalle.

Advertisement

Ga hotunan yadda jama’a suka fito ga hidimar ralin Atiku Abubakar.

Advertisement
Advertisement
Advertisement

Advertisement