Connect with us

Labaran Najeriya

Matasan Jihar Benue sun fusata da ziyarar Buhari a Jihar Benue

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Matasan Jihar Benue sunyi kunar Tsintsiya, Alamar rashin amincewa da Zaben Buhari

Rahoto ta bayar da cewa Matasan Jihar Benue sun fada wa Fillin Wasan Kwallon Kafa da ke a Makurdi, inda shugaba Muhammadu Buhari da Jam’iyyar APC suka gudanar da hidimar neman zabe. Matasan sun fito ne da yawan su tare da tsintsiya a hannun su wai don share bakin jini da shugaba Muhammadu Buhari ya shigo a Jihar da ita.

Muna da sani a Naija News cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya ziyarci Jihar Benue ranar Laraba 6 ga Watan Fabrairun, 2019 da ta gabata don gudanar da hidimar yakin neman sake zabe a zaben tarayya da ke gabatowa a kasar Najeriya a shekara ta 2019.

Bayan barin shugaba Muhammadu Buhari da Jam’iyyar APC a Jihar, Matasan sun fito makil da tsintsiyar su dan share filin da kuma kone tsintsiyar, watau alaman rashin amincewa da shugabancin Jam’iyyar APC.

Ko da shike muna da sani a Naija News da cewa ba shugaba Muhammadu Buhari ne kawai aka wa irin wannan ba, yawancin shugabannan kasar Najeriya sun fuskanci irin wannan zargi da kiyayya.

Karanta Wannan kuma: Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi barazanar cewa duk Kasar Waje da ta sa baki ga zaben Najeriya za ta fuskanci mutuwa.

Kalla: Yadda ‘yan  Najeriya suka bayyana kiyayyar su da tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo