Connect with us

Uncategorized

2019N-Power: Gwamnatin Tarayya sun bayyana lokacin da za a saki fom na N-POWER

 

2019 N-Power

Gwamnatin tarayya ta samu gane da cewa ana rudin wasu da cewa fom na N-Power ta shekarar 2019 ya fito tun watannan baya. Harma wasu sun bayar da kudin su a layin yanar gizon ga mutanen da basu sani ba, wai don taimaka masu da cika fam din.

Bayan gane da wannan, gwamnatin tarayya sun gabatar da cewa a halin yanzu fam din bai fito ba, amma zasu sanar da shi a shafin yanar gizo da N-Power ke amfani da ita kamar yadda aka saba a baya.

A Naija News Hausa, mun yi alkawari da sanar da hakan kuma, da yadda zaka cika fam din idan lokaci ya gabato. Mun bukaci ka bi wannan shafi na mu; Hausa.NaijaNews.Com a kowace lokaci. A nan ne zamu sanar maku da cikakken labari da kuma matakan da za a dauka har ga cika fom din ba tare da samun wata nasara ba.

Mista Afolabi Imoukhuede, Babban shugaba mai taimakawa ga shugaba Muhammadu Buhari wajen samar da ayuka a kasa, ya bayyana a shafin yanar gizon nishadarwa ta Facebookr da cewa lallai gwamnatin tarayya bata bude layin cika fom na N-Power ba tukun na, amma za a yi hakan idan an kamala zaben tarayya ta Najeriya gaba daya.

“Gwamnatin tarayya bata saki fom na N-Power ba tukun na, amma za ta yi hakan bayan an kamala hidimar zaben kasar Najeriya gaba daya” inji fadin Mista Afolabi a layin Facebook da N-Power ke amfani da ita a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2019 da ta gabata.

“Zamu kuma sanar da duk wata mataki akan hakan idan lokaci ya yi na sake cika fom din” inji shi.

Mista Afolabi ya gabatar da hakan ne a yayin da yake mayar da martani ga jita-jita da tambayoyi da mutane ke ta aikawa game da zancen fom na N-Power ta shekarar 2019.

Karanta wannan kuma: Ku dauki kaddarar nasarar Muhammadu Buhari – inji Sultan na Sokoto

Advertisement
close button