Connect with us

Uncategorized

Boko Haram sun kashe Sojoji 23

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Rundunar Sojojin Najeriya sun yi rashin darukai 23 ga ‘yan ta’addan Boko Haram a wata sabuwar hari.

A yau Jumma’a, 22 ga watan Maris 2019, Naija News ta samu rahoton cewa ‘yan ta’addan Boko Haram sun kashe sojoji 23 a wata harin da aka yi wa sojojin a yankin Chadi.

Kamar yadda wani Ofisan Rundunar Sojojin ya bayyana ga manema labarai a yau da cewa abin ya faru ne a missalin karfe daya na safiyar ranar Jumma’a (yau), inda ‘yan ta’addan suka kai hari ga rundunar sojojin da ke a Dangdala, a yankin kasar Chadi.

A halin yanzu ba cikakken bayani akan yadda abin ya faru da abin da ya biyo baya, amma zamu sanar anan shafin idan hakan ya samu.

Karanta wannan kuma: An kashe kimanin mutane 43 a wata harin ‘yan ta’adda a Masallacin New Zealand