Connect with us

Uncategorized

Kalli Jihohin da za a gudanar da Zaben ranar Asabar ta gaba

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

A ranar Alhamis, 21 ga watan Maris da ta gabata, Hukumar gudanar da hidimar zaben kasa (INEC) sun gabatar da Jihohin da za a gudanar da zaben kujerar Gwamnoni da wasu zabanni da aka dakatar a baya.

Kamar yadda hukumar ta sanar a baya da cewa zata kadamar da sauran zabannin a jihohin kasar a ranar 23 ga wata Maris 2019.

Sun gabatar ne a wata takarda da cewa zaben zai kasance ne a Jihohi biyar a kasar.

Kalli tsarin zaben a kasa;

JIHA                               HUKUMOMI                        

Bauchi                           Kananan Hukumomi 14

Benue                            Kananan Hukumomi 22

Plateau                          Kananan Hukumomi  9

Kano                              Kananan Hukumomi 29

Sokoto                           Kananan Hukumomi 22

Ko da shike Naija News Hausa ta gane da cewa akwai jayayya tsakanin Kotun Kara da Hukumar INEC game da zaben Jihar Bauchi. Mun kuma ruwaito a baya da cewa hukumar INEC ta gabatar da yadda zasu kadamar da zaben Jihar Bauchi.