Connect with us

Uncategorized

Wani Matashi ya ci karo da Gidan Jaru bayan da yayi wa ‘Yar Shekara 12 Ciki

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kotun Kara ta Jihar Katsina ta saka wani mutumi mai shekaru 25 ga Kurku da zargin yiwa diyar Makwabcin sa
mai shekaru goma shabiyu ciki.
Naija News Hausa ta samu rahoto da cewa Hussaini Muntari, mutumin da yayi wa yarinyar ciki, mazauni ne na
kauyan Inwala Jangele da ke a karamar hukumar Batagarawa ta Jihar Katsina.

An bayyana da saka matashin a gidan jaru zar sai ga ranar 30 ga watan Afrilu ta shekarar 2019 kamin a ci
gaba da karar a jagorancin babban alkalin Kotun kara ta Jihar Katsina, Hajiya Fadila Dikko.

Naija News Hausa ta gane bisa bayanin ‘Yan Sanda da cewa Muntari, mutumin da ya aiwatar da halin banzan
makwabci ne ga Uban Yarinyar, Mohammed Sani.

Bayan da Malam Sani ya gane da abin da Muntari ya aikata, sai yayi gaugawa da kai karar ga Hedkwatan
jami’an tsaron da ke a yankin Batagarawa.
‘Yan Sanda sun bayyana da cewa Malam Sani bai gane da abin da ke gudana tsakanin Muntari da diyar shi ba
sai har ranar 22 ga watan Janairu 2019 da ya gane da cewa diyar nasa na dauke da juna biyu sakamakon jima’i
da Muntari ke yi da ita.

An kara bayar da cewa Yarinyar da aka yi wa cikin ta bada tabbaci da cewa lallai Muntari ne yayi mata
cikin. “Cikin da ni ke dauke da shi na Muntari ne. Yayi Jima’i da ni sau da dama a cikin dakin shi” inji
Yarinyar.

Insfekta Sani Ado, shugaban Jami’an ‘Yan Sandan yankin, da ke jagorancin karar ya bayyana ga Kotun kara a
ranar Talata da cewa suna kan bincike game da karar.
Ko da shike a halin yanzu, an saka Muntari a gidan jaru har sai ranar da Alkali Dikko ta gabatar ya kai ga
isowa.
Mun ruwaito a baya a Naija News Hausa da cewa Hakilu Saidu, wani manomi mai shekaru 30 ya kashe diyar agolan makwabcin sa da ke da shekaru hudu 4 a Jihar Katsina.