Connect with us

Uncategorized

#BokoHaram: Mutane 5 sun mutu, Kimanin 45 kuma da mugan raunuka a wata Kunar bakin wake

Published

on

at

Advertisement

Kimanin mutane biyar suka rasa rayukan su a wata sabuwar harin ‘yan kunan bakin wake da aka yi a Maiduguri ta Jihar Borno a karshen makon da ta gabata.

Advertisement
Advertisement

Harin ta bar mutane kusan arba’in da biyar (45) da raunuka a yayin da ‘yan ta’addan suka hari wata shiyya da ake ce da ita Muna-Dalti, a garin Maiduguri, babban birni Jihar Borno, a daren ranar Asabar da ta wuce.

Advertisement

A ganewar Naija News, bincike ya bayyana da cewa ‘yan mata biyu ne suka aiwatar da kunar bakin waken.

Advertisement
Advertisement

An bayyana da cewa ‘yan kunar bakin waken sun hari shiyar Muna-Dalti ne da mugayan bama-baman (IEDs)  sanye a jikunan su a daren ranar Asabar.

Advertisement

Shugaban Hukumar (SEMA), Kachalla Usman ya gabatar ga manema labarai da cewa lallai harin da gaske ne, kuma mutane biyu sun mutu a yayin da ake nuna masu kulawa a Asibiti.

Advertisement

“A halin yanzu, ana kan bayar da kulawa ta gaske ga wadanda suka samu raunuka a sakamakon harin a babban Asibitin da ke a Maiduguri” inji Usman.

Advertisement
Advertisement
Advertisement

Karanta wannan kuma: Wani Mahaukaci ya Kashe Dan Sanda a Jihar Kwara

Advertisement