Connect with us

Uncategorized

Boko Haram: An Kashe mutane 7 da Sojoji 3 a garin Molai ta Jihar Borno

Published

on

at

Advertisement

Boko Haram sun kai sabuwar hari a Jihar Borno da dauke rayukan mutane kimanin 10

Naija News Hausa ta karbi rahoto cewa ‘yan ta’addan Boko Haram sun hari yankin Molai da ke mafitar garin Maiduguri, da maraicen ranar Talata da ta wuce, inda suka kashe kimanin rayuka goma.

Advertisement
Advertisement

Wannan abin ya faru ne a garin Molai da ke a karamar hukumar Jere ta Jihar Borno. 

Advertisement

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya da cewa wasu ‘Yan hari da Makami sun kashe wani Sarki a kauyan Balle da ke yankin Jihar Sokoto, inda suka kone Ofishin Jami’an tsaro da motocin su biyu a ranar Talata da ta wuce.

Advertisement
Advertisement

A wannan hari da aka kai a garin Molai, an sanar da cewa fiye da mutane 100 ne aka bari huntu da rashin gidaje a yayin da ‘yan ta’addan suka kone masu gidajen kwanan su.

Advertisement

Ba gidaje kawai ba, mazaunan wajen sun bayyana da cewa ‘yan ta’addan sun kone rukunonin tsaron rundunar Sojoji da ke a shiyar.

Advertisement

Mallam Isa Kagama, wani mazaunin kauyan Balle ya bayyana ga manema labarai cewa sun rasa rayukan mutanen su bakwai (7) a harin.

Advertisement
Advertisement

“Kimanin mutane Goma (10) ne ‘yan ta’addan suka kashe, Sojoji Ukku da kuma mutane 3 daga kauyan Maiboriti, mutum 4 kuma daga kauyan Molai.”

Advertisement

“A halin yanzu ‘yan ta’addan sun barmu da rashin gidajen barci, kayakin mu duk sun kone, harma sun lallace Injimi Wutan Lantarki da ke samar da wutan lantarki ga dukan garin Maiduguri; ku dube mu, duk mun lallace.” inji Malam Isah.

Advertisement

Ko da shike manema labarai, a lokacin da aka karbi wannan rahoton ba a samu karban bayani daga wata hukumar tsaro ba, amma watakila hakan zai faru idan an jima.

Advertisement
Advertisement
Advertisement

KARANTA WANNAN KUMA; Mutuwa rigan Kowa! Maman Sanata Dino Melaye ta riga mu zuwa Gidan Gaskiya

Advertisement