Connect with us

Uncategorized

Rundunar Sojojin Najeriya sun ribato Mata 29 da Yara 25 daga rukunin Boko Haram

Published

on

at

Advertisement

Rukunin Rundunar Sojojin Najeriya ta Operation LAFIYA DOLE sun gabatar da ribato mata 29 hade da ‘yan yara 25 a wata kangin ‘yan ta’addan Boko Haram da ke a Jihar Borno.

Advertisement
Advertisement

Bisa ganewar Naija News Hausa, Rundunar Sojojin sun samu nasarar hakan ne a wata yawon hadin kai da suka yi na ‘yan bangan Jihar Borno a ranar 11 ga watan Mayu da ta wuce, inda suka fada wa kauyan Ma’allasuwa da Yaga – Munye ta Jihar Borno da binciken ‘yan ta’adda.

Advertisement

Ko da shike ‘yan ta’addan Boko Haram din basu jira isar rundunar Sojojin ba, sai suka hari daji da gudu, suka kumar bar tarin mutane 54 da ake zaton cewa an sace su ne daga filin hari.

Advertisement
Advertisement

A cikin mutane 54 da ‘yan ta’addan suka bari, an taras da samun tarin Mata 29 da kuma kananan yara, maza da mata 25.

Advertisement

A cikin yawon zagayen Rundunar Sojojin, an bayyana da cewa sun taras da Motocin Yakin ‘yan Boko Haram biyu a Zari – Kasake da kuma kauyan Jumachere a karamar hukumar Mobbar ta Jihar Borno, sun kuma rushe su da kayakin da ke a cikin su.

Advertisement

Advertisement
Advertisement

A garin hakan ne kuma suma taras da wani da ake diba da jami’a in tsaron ‘yan sanda masu yawo (Mopol), Sergeant Markus John, mai lamba kaki- PNo 383106.

Advertisement

Rundunar Dakarun Tsaron sun bayar da cewa sun ci karo ne da shi a rukunin tsaron su da ke a Njimtilo ta shiyar hanyar Maiduguri zuwa Damaturu. An gane shi ne da Miyagun Makamai kamar (magazines 2), da kuma wasu kayakin yaki da dama cikin jakkar da yake tafiya da ita zuwa Jihar Legas.

Advertisement
Advertisement

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya cewa Sojojin Najeriya sun kame masu Kira da Samar da Makami ga ‘yan Ta’adda a Kontagora (Neja) da Katsina

Advertisement
Advertisement