Connect with us

Uncategorized

#Ramadan: Yashi ya rufe wasu Yara Shidda a Jihar Kano, Uku sun mutu daga cikin su

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Ma’aikatan Hukumar Yaki da Gobarar Wuta na Najeriya (Fire Service), sun ribato ran wasu kananan yara shidda da yashi ya rufe da su a kauyan Kuka ta karamar hukumar Gezawa, a Jihar Kano.

Ko da shike abin da takaici, Kakakin yada yawun Hukumar ‘yan Fire Service na Jihar Kano, Malam Saidu Mohammed ya bayyana ga manema labaran NAN a ranar Talata da cewa Malaman Asibitin Gezawa sun bashi tabbacin cewa uku daga cikin yaran da aka tono daga cikin yashi sun mutu.

“Mun karbi wata kirar gaugawa daga rukunin mu ta Gezawa daga wani mutumi mai suna Malam Muktar, a missalin karfe 11:59 na safiya da cewa yashi ya rufe wasu yara shidda a wajen da suke tonon yashi”

“Da jin rahoton, sai Ma’aikata suka yi wuf zuwa wajen, a isar su kuma suka tono yaran, aka kuma isar da su a asibiti don binciken lafiyar jikunansu” inji Saidu.

Ga sunayan yaran a kasa kamar yadda aka bayar ga manema labarai;

  • Abdullahi Abdul         –  Da shekara 12 da haifuwa
  • Aminu Isa                   –  Da shekara 13 da haifuwa
  • Bashir Umar               –  Da shekara 13 da haifuwa
  • Naziru Rabiu              –  Da shekara 17 da haifuwa
  • Usman Garba             –  Da shekara 14 da haifuwa
  • Zakari Dandolo          –  Da shekara 12 da haifuwa

Mista Saidu ya kara da cewa sauran yara ukun na Asibitin Gezawa ana basu cikakken kulawa don ribato ran su.

“mun riga mun mika gawakin yara ukun ga Wakilin Kauyan Gezawa, sauran ukun kuma suna asibiti wajen kulawa, a yayin da zamu ci gaba da bincike akan yadda al’amarin ya faru” inji bayanin Mista Saidu a ranar Litini da ta gabata.

KARANTA WANNAN KUMA: Mazauna Jihar Kaduna sun kai hari a babban hanyar Kaduna-Zaria da Kaduna-Lagos, sun katange manyan hanyoyin da kone-konen tayoyi da wuta don nuna rashin amincewar kisan wani da ‘yan sanda suka yi.