Connect with us

Uncategorized

An gane da Gawar wata Yarinya a cikin Rijiya a Jihar Kano

Published

on

at

Advertisement

Hukumar Yaki da Gobarar Wuta ta Jihar Kano, ta sanar da cewa ranar Talata da ta gabata sun gane da gawar wata ‘yar karamar yarinya mai shekaru 11 a ciki rijiya.

Advertisement
Advertisement

An gano gangan jikin yarinyar ne da aka bayyana sunan ta da Fatima Abdullahi a cikin wata Rijiya a shiyar Zaura Ganduje, a karamar hukumar Dawakin Tofa, Jihar Kano.

Advertisement

Kakakin yada yawun, Alhaji Saidu Mohammed, ya bayyana ga Kungiyar Manema Labaran Najeriya (NAN) a Jihar Kano cewa sun gane da hakan ne a safiyar ranar Talata da ta wuce.

Advertisement
Advertisement

A bayanin Mohammed da manema labaran NAN, ya bayyana cewa hukumar su ta karbi kirar gaugawa ne daga  Dawanawu cewa wata karamar yarinya ta fada a cikin rijiya.

Advertisement

Ya kara da cewa lallai kamin isar ma’aikata a wajen, yarinyar ta riga ta mutu.

Advertisement

Ya kuma bayyana cewa bayan da hukumar ta gane da gawar yarinyar, sun dauke ta da mika ta ga wakilin garin Zaura, Alhaji Idris Shua’ibu.

Advertisement
Advertisement
Advertisement

“Har yanzu ana kan bincike ga sanadiyar da ya kai yarinyar a cikin rijiyar” inji shi.

Advertisement