Connect with us

Uncategorized

An kafa kai ga Hidimar Zaben shugaban sanatocin Najeriya

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kamar yadda muka sanar a Naija News Hausa a baya da cewa a yau Talata, 11 ga watan Yuni 2019, za a kadamar da zaben shugaban sanatocin Najeriya da kakakin yada yawun gidan Majalisar Wakilai, hidimar a haka ta riga ta fara.

Dan takaran kujerar shugaban gidan Majalisa, Ali Ndume yayi gabatarwa da gargadin ‘yan Majalisa da su tabbatar da cewa sun bi zuciyar su a hidimar.

“Ina mai gargadi da cewa kowa zai bi zuciyar sa ga zaben, zai fi kyau kuma muyi zaben da diban gaba, jagoranci mafi kyau. Na bada gaskiya da cewa duk wanda kuka zaba, zabin Allah ne” inji Ndume.

A haka Naija News Hausa na sanar da cewa an fara zaben…. zamu kuma sanar da duk wata ci gaba da zai biyo bayan zaben…