Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 11 ga Watan Yuni, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 11 ga Watan Yuni, 2019

1. APC, Gwamnoni da ‘yan Majalisa sun bada goyon baya ga Lawan da Gbajabiamila

Manyan jigo da shugabannan Jam’iyyar APC, Gwamnonin Jiha da ‘yan Majalisar Dattijai da ke wakilci a Jam’iyyar APC sun bada goyon baya ga Ahmed Lawan da Femi Gbajabiamila a zaman shugaban Sanatocin Najeriya da kakakin gidan Majalisa.

Haka kazalika aka bayyana goyon baya ga Sanata Ovie Omo-Agege da Idris Wase a matsayin mataimakin shugaban sanatoci da mataimakin kakakin yada yawun majalisa.

2. Shugaba Buhari ya rattaba hannu ga bil na hidimar ranar Dimokradiyya, 12 ga Yuni

Shugaba Muhammadu Buhari ya rattaba hannu ga bada hutu ranar 12 ga watan Yuni 2019 don hidimar ranar Dimokradiyya.

Naija News Hausa ta gane da rahoton ne bisa sanarwa da aka bayar daga bakin Sanata Ita Enang, mai wakilcin shugaba Buhari a al’amarin gidan Majalisar Dattijai.

3. Kotu ta kafa baki ga hidimar karar Atiku da Buhari

Kotun Neman Yanci da ke tafiyar da karar Atiku Abubakar da Shugaba Muhammadu Buhari ga zancen zaben 2019, a birnin Tarayya, Abuja, a ranar Litini da ta gabata, sun tada zancen karar.

A yayin da ake kan zancen, kotun ta janye kara ta Uku da Jam’iyyar Coalition for Change suka gabatar a baya akan hidimar zaben watan Fabrairu 2019.

4. INEC ta gabatar da lokacin da zata dauki mataki akan Okorocha

Hukumar Gudanar da Hidimar Zaben kasar Najeriya (INEC) sun bayyana da cewa a yau Talata, zata kara bincike da binbini akan ko watakila zata iya bayar da takardan yancin wakilci ga Rochas Okorocha.

Naija News ta fahimta da cewa za a gabatar da sabin ‘yan Majalisar Dattijai a yau, wanda ya nuna da cewa Okorocha ba zai samu damu kasancewa a ciki ba, don ba a bayar da takardan shiga Majalisar ba a gareshi.

5. Gwamna Sanwo-Olu ya nada Alogba a matsayin babban Alkali a Legas

Gwamnan Jihar Legas, Mista Babajide Sanwo-Olu ya gabatar da Alkali Kazeem Alogba a matsayin babban alkali da zai wakilci Kotun Koli ta Jihar Legas.

Naija News ta samu ganewa da hakan ne bisa wata sanarwa da aka bayar bayan da Gwamna Sanwo-Olu ya sanya Alkalin a ranar Litini da ta wuce.

6. Adebo Ogundoyin ya lashe kujerar kakakin yada yawun Majalisa a Jihar Oyo

Dan shekara 32 ga haifuwa, Mista Adebo Ogundoyin ya ci nasara da lashe zaben zama kakakin yada yawun gidan Majalisar Jihar Oyo.

A fahimtar gidan labaran nan tamu, Ogundoyin ya karshe karatun sa ne daga makarantar Jami’a babba ta Babcock University, haka kuwa ya dace da zama kakakin yada yawun Majalisar Jihar ba tare da jayayya ba.

7. Garba ya maye gurbin Bulkachuwa ga karar neman yanaci tsakanin Buhari da Atiku

Alkali Mohammed L. Garba ya maye gurbin tsohon jagoran Kotun neman yanci, Zainab Bulkachuwa, a hidimar karar jayayya da neman yanci tsakannin shugaba Muhammadu Buhari da Alhaji Atiku Abubakar akan zaben watan Fabrairu.

Naija News na da sanin cewa a da, Mista Garba ne ke jagorancin kotun kara da ke a wata yankin Jihar Legas.

8. Rundunar Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 9

Rundunar Sojojin Najeriya sun gabatar da cewa sun kashe mutane tara da aka gane da kasancewa cikin rukunin ‘yan ta’addan (ISWAP).

Bisa wata bayani da aka bayar daga bakin Col. Sagir Musa, Daraktan Rundunar Sojoji a lamarin sadar da labarai, ya bayyana da cewa sojoji sun ci nasara ga kashe mutane 9 da ke da hakin ta’addanci a kasar.

Ka samu kari da cikkaken Labaran Najeriya a shafin Hausa.NaijaNews.Com