Connect with us

Uncategorized

Kalli Jerin Shugabanan Sanatoci da suka yi jagoranci a Najeriya tun shekarar 1960

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Mun sanar a Naija News Hausa ‘yan sa’o’i da suka wuce da hidimar zaben sabon shugaban Gidan Majalisar Dattijai na 9.

Hidimar da aka yi a yau Talata, 11 ga watan Yuni 2019, ya karshe da murna ga Jam’iyyar APC, a yayin da dan takaran su a kujerar shugabancin gidan Majalisar, Ahmed Lawan da mataimakin sa, Ovie Omo-Agege suka lashe tseren zaben.

Hakan ya tabbata ne bayan da suka fiye ‘yan adawar su daga Jam’iyyar PDP da yawan kuri’u a zaben.

Tun daga shekarar 1960 da kasar Najeriya ta karbi yancin dayantakewa a shugabanci, kasar har ga wannan shekara ta karbi shugabancin shugabannai 14 a Majalisar Dattijai, daga Jam’iyu daban-daban.

Kalli jerin sunayan su a kasa da shekarun da suka yi jagoranci;

Sunan Shugabannan Sanatoci Sa’a/Shekarar mulki Jam’iya
Nnamdi Azikiwe 1960 NCNC
Dennis Osadebay 1960-1963 NCNC
Nwafor Orizu 1963–1966 NCNC
Joseph Wayas 1979–1983 NPN
Iyorchia Ayu 1992–1993 SDP
Ameh Ebute 1993 SDP
Evan Enwerem 1999 PDP
Chuba Okadigbo 1999–2000 PDP
Anyim Pius Anyim 2000–2003 PDP
Adolphus Wabara 2003–2005 PDP
Ken Nnamani 2005–2007 PDP
David Mark 2007-2015 PDP
Bukola Saraki 2015-2019 PDP
Ahmed Ibrahim Lawan 2019 – present APC

KARANTA WANNAN KUMA; Ba zamu bada Filin kiwo ba ga Fulani a Jihar mu – Kungiyar Iyamirai (Ohanaeze) sun yi barazanar haka.