Connect with us

Uncategorized

‘Yan Kunar bakin wake sun kashe mutane fiye da ashirin a wata tashin Bam a Borno

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Rundunar Sojojin Najeriya sun sanar da cewa fiye da mutane 20 wasu ‘yan kunar bakin wake suka kashe da tashin bam a wata gidan kallon wasa da ke a Konduga, nan Jihar Borno.

Bisa rahoton da aka bayar ga Naija News Hausa, An sanar da cewa kimanin mutane 30 suka samu raunuka daban-daban a harin.

Mumunar lamarin ya faru ne bayan da wasu mutane biyu, mace da namiji da ake zargi da zaman ‘yan ta’addan Boko Haram, da ke dauke da kayan bam na (IED) suka hari wani gidan kallon wasa da ke gaba ga wata Asibitin Mandarari, a karamar hukumar Konduga, missalin karfe Tara na daren ranar Lahadi da ta gabata.

Ko da shike an samu cin karo da wata ‘yar mace kuma da ke dauke da kayan bam na IED, da aka gane da ita sai aka kame ta tun bata fashe da bam din ba, aka kuma mikar da ita ga rundunar tsaron sojojin.

Ka tuna da cewa mun sanar a Naija News Hausa a baya cewa ‘Yan Hari da Bindiga sun sace Wakilin Garin Labo a Jihar Katsina