Connect with us

Uncategorized

Kalli abinda Shugaban Majalisar Dattijai, Lawan ya fada game da Albashin ‘yan Majalisai

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shugaban Majalisar Dattijai, Dokta Ahmad Lawan, ya ce babu wani wata kari ko albashin boye ga ‘yan majalisar dokokin kasar kamar yadda aka zayyana a wasu sassa.

Lawan ya gabatar da wannan bayanin ne a yayin da mambobin Majalisar Dattijai suka kai masa ziyara a ofishinsa a birnin Abuja ranar Talata.

A yayinda yake cikin bayanin da ba da la’akari ga zancen kudin kari a boye da ake zargin majalisar da ita, ya bayyana cewa albashin sa da ta kowane dan majalisar bai wuce N750,000 ba.

“Abin da nake so in jaddada a nan shi ne cewa ban taɓa yin imanin cewa akwai wani abu a Majalisar Dattijai da ake kira albashin Jombo (kari/boye) ba”

“A Majalisar Dokoki da Wakilai, kowa na karban daidai albashin sa ne, ni kuma ina karbar Naira Miliyan Dari Bakwai da Hamsin (N750,000) ne a matsayin albashi na.

“Amma dole ne inyi aiki a matsayin Sanata, ya kuma dace Ofishi na ya sami kulawa da ta dace” inji shi.

Sanata Lawan ya kuma yi alkawarin cewa Majalisar zata kasance a bude ga kowa don cin nasara a halartar da ayyukan majalissar, musamman ma a bangaren kudade.

KARANTA WANNAN KUMA;  Hukumar NAHCON ta rage ga Kudin zuwa Hajj ta 2019