Connect with us

Uncategorized

Gidan Sama mai Tsani Uku ya rushe da Mutane ciki a Jihar Legas (Kalli hotuna)

Published

on

at

Advertisement

Naija News Hausa ta karbi rahoton yadda wata gidan sama mai jeri Uku ya rushe da mutane 12 da raunuka a Jihar Legas.

Advertisement
Advertisement

Bisa rahoton da aka bayar ga manema labarai, hakan ya faru ne a daren ranar Laraba da ta gabata a shiyar Fagba, a Jihar Legas.

Advertisement

Babban Ofisan Hukumar Kulawar Gaggawa ta Jihar Legas (LASEMA), Dokta Olufemi Oke-Osanyintolu, ya kara bada haske ga alamarin, da fadin cewa “Ina sanar da tabbatar maku da rushewar gidan sama mai tsani Uku a nan shiyar K Farm, Fagba, hanyar da ta zagaya bawan Iju”

Advertisement
Advertisement

Ya kara da cewa lallai ana kan aiki ne a gidan a yayin da ya rushe da mutane ciki. Ko da shike ya bayyana da cewa mutanen da suka sami raunuka na karban kulawa a wata asibitin da ke a shiyar.

Advertisement

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da rushewar wata gidan sama ta rushe a Jihar Legas

Advertisement

Ko da shike a gidan sama mai tsani ukun, ba rahoton cewa ko kila wani ya mutu a rushewar gidan, amma da tabbacin mutane goma shabiyu da raunuka.

Advertisement
Advertisement

“Za a karkare rushe dukan banaren ginin da ya saura tsaye don hanna shi fadowa ba daidai ba da kuma magance matsalar kara wata mumunar faduwa” inji Dokta Olufemi.

Advertisement
Advertisement

KARANTA WANNAN KUMA; Dalilin da ya sa aka jefa wani Malamin Islamiyya a Kurkuku

Advertisement