Connect with us

Uncategorized

Kalli Abin da Sojoji suka yiwa wani Sojan Karya da aka kama da zaluntar mutane

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Sojojin Najeriya sun kame wani Sojan Karya

Wani matashi da ya saba zaluntar mutane a sunan cewa shi soja ne ya fada a hannun Sojojin Gaske a Jihar Osun.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa matashin da har yanzu ba a gane da ainihin sunansa ba, ya saba tsorata da zaluntar Dalibai a Makarantan Fasaha ta Igbajo Polytechnic a Jihar Osun.

Hausawa sun ce “Kulluma na barawo amma rana daya ga mai kaya”, Sojan karyan ya fada a hannun rundunar Sojojin Jihar, inda suka ci mutuncin sa a fili ga ganin jama’a.

An bayyana da cewa matashin kan sanya kakin Sojoji ne, sai ya haura ga shiyar Makarantan Jami’ar, daga nan kuma sai yayi ta cin mutunci dalibai a sunan Soja.

Sojojin kuma da suka kama shi sai suka Isgila shi da yi masa mugun duka a gaban jama duka.

Kalli Bidiyon a kasa;

https://www.instagram.com/p/BzcbvWkH-Ww/?utm_source=ig_embed

KARANTA WANNAN KUMA; Bayanin tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar game da Sanata Elisha Abbo da ya zalunci wata Mata a birnin Abuja