Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Litini, 22 ga Watan Yuli, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Litini, 22 ga Watan Yuli, 2019

1. Anyi karar Buhari, Tsohin shugaban kasa da wasu manya a kasar Najeriya ga Hukumar ICC

Hukumar Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP) ta gabatar da wata zargi a gaban Alkalin Kotun International Criminal Court (ICC), Malama Fatou Bensouda, da bukatar ta da binciken rashin kulawa da shugabancin kasar ta nuna ga yaran da basa a makaranta a kasar Najeriya.

Hukumar SERAP a cikin karar, ta gargadi Alkali Bensouda da binciken rashin jinkirtan Manya a kasar Najeriya akan al’amarin da tsawon shekaru da suka gabata.

2. Boko Haram: Hukumomin Tsaro sun gano da inda aka katange Masu taimaka wa kiwcon lafiya da aka fyauce a baya

Hukumomin tsaro da ta kunshi hukumar rundunar Sojojin Najeriya sun gano da inda mutanen da aka bayyana da bacewa a baya suke.

Naija News ta fahimta da cewa mutanen sun bace ne tun kwanakin baya a wata hari da ‘yan ta’addan Boko Haram suka kai a shiyar da su ke.

3. Karya Buhari yayi game da katange El-Zakzaky – inji ‘Yan Shi’a

Kungiyar Cigaban Musulunci ta Najeriya (IMN) da aka fi sani da ‘Yan Shi’a sun bayyana da cewa ƙaddara da tsirar shugaban kungiyar su, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, na a hannun shugaba Muhammadu Buhari.

Naija News ta fahimta da cewa shugaba Buhari ya fadawa ‘yan shi’a a ranar Jumma’a da ta gabata da cewa su bar kotu da gabatar da hukunci ga shugabansu.

4. Majalisar Dattijai sun gayawa shugaba Buhari lokacin da zai bayar da Jerin sunan Ministoci

Majalisar Dokoki ta Najeriya sun gargadi shugaba Muhammadu Buhari da bayar da jerin sunayan Ministoci da zasu yi wakilci a shugabanci sa ta ‘Next Level’ kamin ranar Jumm’a ta gaba.

Naija News ta fahimta da cewa Babban rukunin Majalisar Dattijai zasu shiga hutun su ta shekara da shekara kamar yadda suka saba daga ranar Jumma’a 26 ga watan Yuli har zuwa ranar 26 ga watan Satunba.

5. Oyegun ya gargadi Oshiomhole da barin kunyatar da Jam’iyyar APC

Tsohon Ciyaman Tarayyar Jam’iyyar APC, John Odigie Oyegun, ya gargadi Adams Oshiomhole da janyewa daga kunyatar da Jam’iyyar.

Naija News na da sanin cewa a halin yanzu Oshiomhole nada jayayya da Gwamnan Jihar Edo, Godwin Obaseki, akan shugabancin Jam’iyyar APC ta jihar.

6. ‘Yan Kungiyar Biafra sun aika sakon gargadi ga Miyetti Allah

Kungiyar Matasan ‘yan Biafra da ake kira ‘Biafra Nations Youth League’, BNYL ta gargadi Makiyaya Fulani da barin yankin Kudu ko kuma su fuskanci duk abin da ya biyo da baya.

Naija News ta tuna da cewa Miyetti Allah Kautal Hore ta umurci makiyaya Fulani da su kare kansu daga duk wata hari a kuducin kasar.

8. COZA: ‘Yan Sanda sun yi bayani game da bukatar Busola da Timi Dakolo da bayani a ofishinsu

A ranar Asabar da ta wuce, Hukumar ‘Yan Sandan Najeriya sun bayyana da cewa lallai sun samar da takardan bukatar bayani daga bakin Busola da Timi Dakolo.

A ganewar gidan labaran nan tamu, akwai ganewa da cewa ‘yan sandan sun bukaci hakan ne don neman bayani akan matsalar da ke tsakanin matar Timi Dakolo da Faston da ke jagorancin Ikilisiyar COZA.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNewsHausa