Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 13 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 13 ga Watan Agusta, 2019

1. Gwamnatin Tarayya ta ba da Dalilin da yasa ba ta aiwatar da biyan kankanin Albashi ba

Bayan barazanar shiga zanga-zanga da kungiyar kwadago ta yi, Gwamnatin Tarayya ta danganta jinkirin aiwatar da sabon albashi mafi karancin ga Ma’aikata da sanadiyar wasu bukatu marasa manufa da kungiyar kwadago ta gabatar.

An bayyana wannan zancen ne a bakin, Richard Egbule, Shugaban Hukumar Albashi ta Kasa, da Hukumar Inshorar a yayin wata tattaunawa da yayi da NAN a ranar Litinin da ta wuce.

2. Shugabancin Kasa ta Bayyana Abinda Shugaba Buhari keyi Game da Rikicin Sojoji da ‘Yan Sanda

Shugabancin kasar ta bayyana da cewa akasin ganewa da imanin wasu a kasar na nunin cewa Shugaba Muhammadu Buhari bai damu da rikicin da ya afku tsakanin jami’an ‘yan sanda da sojoji ba.

Ka tuna kamar yadda Naija News ta sanar a baya da cewa darukan sojojin Najeriya sun kashe wasu jami’an ‘yan sanda a jihar Taraba wadanda ke biye da wani jagoran ‘yan fashi, Alhaji Hamisu.

3. El-Zakzaky da Matar sa sun tashi daga Najeriya zuwa kasar Turai

Shugaban kungiyar Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN), wanda aka fi sani da ‘Yan Shi’a, Shaikh Ibraheem El-Zakzaky da matarsa, Zeenat, a daren ranar Litinin din nan, sun bar kasar zuwa Indiya don binciken lafiyar jikinsu.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa sun tashi zuwa India ne a kan jirgin Emirate daga filin jirgin sama ta Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

4. Dalilin da yasa ya zan dole ga EFCC ta Kama Buhari da Tinubu – Omokri

Reno Omokri, tsohon mai mataimaki ga hidimar aiki ga tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya ce ikirarin da Timi Frank ya bayar ya tabbatar da cewa ya karyata Jonathan.

Ya kara da cewa furucin Frank, tsohon Sakataren yada labarai na Jam’iyyar APC na kasa ya tabbatar da cewa tsohon Shugaba Jonathan mai Imani ne.

5. Abinda ya zan Dole da yi ga ‘Yan Najeriya  – Bola Tinubu

Jagoran jam’iyyar APC na kasa baki daya, shugaba Bola Tinubu, ya ce dole ne ‘yan Najeriya su sadaukar da kansu ga ci gaba da karuwar kasar.

Naija News ta gane da cewa Tinubu yayi wannan tsokaci ne yayin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala sallar Eid-el-Kabir.

6. Abin da Shugaban Guinea ya fada wa Buhari game da Tinubu

Naija News Hausa ta fahimta bisa rahotannai da cewa daya daga cikin dalilin ziyarar shugaban kasar Guinea, Shugaba Alpha Conde ga Buhari ita ce neman dama ga Cif Bola Tinubu don maye gurbin Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2023.

Ka tuna da cewa Conde ya halara a garin Daura na jihar Katsina a karshen mako don ziyarar shugaba Buhari yayin da shugabannin kasashen Afirka biyu ke bikin zagayowar Sallar Eid-El-Kabir.

7. Rundunar Sojojin Najeriya ta Kori wani Jarumi don Lalata da wata Daliba Jami’a

Sunday Adelola, mai igiyar daukaka ta Lance Corporal ta sojojin Najeriya wanda aka kama da yi wa wata daliba makarantar Jami’a ta Adekunle Ajasin Akungba Akoko fyaden Dole.

Naija News ta fahimci cewa an mika Mista Adelola ga ‘yan sanda don bincike tare da gurfanar da shi nan take rundunar ta kore shi.

8. Kungiyar Kwadago ta Najeriya ta gabatar da sabon gargadu  ga Gwamnati

Kungiyar kwadago ta kasa (TUC) ta gargadi gwamnatin tarayya da ta daina jinkiri da biyan sabon albashi mafi karanci ga Albashin ma’aikatan Najeriya.

Shugaban TUC na jihar Ekiti, Sola Adigun, wanda ya yi wannan kiran, ya roki Gwamnatin Tarayya da kar ta kara ga jinkirtar biyan albashin, da kuma kada su wuce ranar Laraba, 14 ga Agusta 2019.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNewsHausa