Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 20 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 20 ga Watan Agusta, 2019

1. Oyo-Ita ya kaurace da kasance hidimar Ilimantar da sabbin Sanatoci da Buhari ya jagoranta

Shugaban ma’aikatan kwadagon na tarayya, Winifred Oyo-Ita bata halarci taron Ilimantar da sabbin Ministoci wanda Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta na shekarar 2019.

Naija News ta tuna da cewa Hukumar kare tattalin arzikin kasa da yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta tuhumi Oyo-Ita a makon da ya gabata kan zargin almundahana da rashawa na kudi N3b.

2. Kungiyar NASU, SSANU sun fara Yajin Aiki a dukan fadin Kasar Najeriya

Wakilan kungiyar Malaman Jami’o’in da ba sa koyarwa (NASU) da kuma Manyan Ma’aikata na Jami’o’in Najeriya (NASU) sun fara yajin aiki na kwanaki biyar.

Kwamitin Ayyuka na NASU da SSANU wadanda suka ba da umarnin yajin aikin sun bayyana cewa sun yi hakan ne bayan da Gwamnatin Tarayya ta kaurace da bin gargadin da aka basu da Korafin kwanaki 14.

3. Abin da Shugaba Buhari Ya gayawa sabbin Ministoci a Lokacin Jawabi

A ranar Litinin din da ta gabata ne Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar da wa’adin shugaban kasa ga wadanda aka zaba ga kujerar ministoci, tare da sauran manyan ma’aikatun gwamnati.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa wannan hidimar anyi ta ne don kafada Ministocin da zasu yi aiki tare da Shugaban kasa nan da shekaru hudu masu zuwa, tare da tantance matsayin kasar a 2015 zuwa inda take a yau da kuma tsara hanya don ci gaban kasar nan gaba.

4. IPOB na Barazanar wulakanta Buhari da Buratai

Bayan harin da aka kaiwa tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ike Ekweremadu, ‘Yan asalin kasar Biafra, sun yi barazanar wulakanta Shugaba Muhammadu Buhari a duk lokacin da ya fita daga Najeriya zuwa kasar Turai.

Kungiyar a cikin sanarwar da ta fitar ta kuma yi barazanar cewa za ta wulakanta Shugaban Hafsun Sojojin Najeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai.

5. Shugabancin APC na Liyafa cikin Cin Hanci da Rashawa – Timi Frank

Tsohon Mataimakin Kakakin yada Yawun Jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Timi Frank, ya bayyana cewa akasarin ‘yan Najeriya suna ganin yadda jagorancin Gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ke rawa tsirara da liyafa cikin Cin Hanci da rashawa a gida da kuma na hadayyar kasa baki daya.

Wannan bayanin Mista Frank ya biyo ne bayan rahoton da Gwamnatin Amurka ta bayar wanda ya la’anci gwamnatin Buhari bisa ci gaba.

6. Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Martani game da Yin Jima’i a BBNaija

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta fid da kara ga Hukumar Watsa Labarai da Nishadi ta Kasa (NBC) game da wasan kwaikwayon soyayya mai ban sha’awa da ake yi mai taken “Big Brother Naija”.

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta cimma matsaya tare da Startimes don gabatar da wani shiri da zai musanya BBNaija wanda zai yada da kuma karfafa al’adun kasar Najeriya.

7. Kotu ta dakatar da AGF, ICPC Daga Kwace kayan Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Yari

Tsohon Gwamnan jihar Zamfara, Abdulazeez Yari ya samu nasarar umarnin Kotu ta kiyaye shi daga cin hanci da rashawa da kuma wasu kungiyoyi masu alaka da shi (ICPC).

Naija News ta tuna cewa a a baya Bankin Gwamnan da ke a Polaris da bankin Zenith sun karbi izinin kotu na rufe Asusun Gwamnan bayan da wata rukunin hukumar tsaro ta (EFCC) ta hari gidansa da bincike a makon da ta gabata.

8. Gobara ta lalata kasuwar Katangowa A Legas

Gobarar ta Barke a wani sanannen kasuwar da ake kira Katangowa inda a ke sayar da tsohin kayaki a karamar hukumar Agbado / Okeodo a nan jihar Legas, a kan hanyar Legas-Abeokuta Expressway.

Naija News ta fahimci cewa barkewar gobarar da ta fara da misalin karfe 3.15 na safiya ta lalata tsawan wasu shagunan suttura da ke a cikin kasuwar a gaban babban masallacin Juma’a na kasuwar.

Ka sami kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa