Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Laraba, 21 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Laraba, 21 ga Watan Agusta, 2019

1. ‘Yan sanda sun sake kama Babban Shugaban Barayi na Taraba Hamisu Wadume

Rundunar ‘yan sanda ta Najeriya (NPF) a ranar Talata da ta gabata, ta tabbatar da sake kame babban dan ta’adda da shugaban barayi a jihar Taraba, Alhaji Hamisu Bala Wadume.

Tabbacin hakan ya  samu ne bisa wata sanarwa da Kakakin Jami’an tsaro, Frank Mba, ya aika wa Naija News da cewa ‘yan sanda sun ci nasara da sake kama Wadume a cikin daren Litinin din nan a inda yake buya, nan Layin Mai Allo Hotoro na jihar Kano.

2. Kotun Koli ta yanke hukunci a kan Atiku da Jam’iyyar PDP

Kotun koli ta yi watsi da Wata kara da jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da dan takarar shugaban kasa a zaben 2019, Atiku Abubakar, suka shigar.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa matakin kotun ya bayyana rashin amincewa da bukatar Jam’iyyar PDP da Atiku Abubakar.

3. EFCC ta Hari Gidan Ambode

Hukumar Yaki da yi Cin Hanci da kare Tattalin Arziki Najeriya (EFCC) a ranar Talata, sun kai hari da mamaye gidan Mista Akinwunmi Ambode, tsohon Gwamnan Jihar Legas da ke a Epe.

Ko da shike Naija News ta fahimta da cewa mazauna yankin Epe sun hari hukumar da hanna su aiwatar da gurin su.

4. Diezani ta La’anci Hukumar EFCC a kan fada wa Gidanta

Tsohuwar Ministar Albarkatun Man Fetur, Diezani Alison-Madueke, ta kalubalanci Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da kare Tattalin Arzikin kasa (EFCC), game da dauke kayan ado da kwalliya masu tsadar gaske na kimanin dala miliyan $40m.

Naija News Hausa ta gane da bayanin Diezani ne bisa wata kara wacce aka gabatar a madadin ta ta bakin lauyan ta, Farfesa Awa Kalu (SAN).

5. Abin da EFCC ta ce game da harin gidan Ambode

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da kare Tattalin Arzikin kasa (EFCC), ta mayar da martani kan zancen cewa hukumar a ranar Talata, ta kai samame da hari a gidan tsohon gwamnan Legas, Akinwumi Ambode, a nan Epe.

Hukumar ta bayyana da cewa ba wai sun hari gidan Ambode ba ne don wata abu amma don binciken sa akan wata zargi.

6. Shugaba Buhari ya sake nada Femi Adesina, Garba Shehu da wasu a rukunin sa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Femi Adesina a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkar yada labarai a layin yanar gizo.

Naija News ta gane da cewa Shugaba Buhari ya kuma sake nada Garba Shehu a matsayin Mataimaki na musanman akan yada labarai a layin yanar gizo.

7. Mazauna Epe sun katange Hukumar Tsaro da shiga gidan Ambode

Wasu mazauna shiyar Epe sun tsaya kai tsaye da dakatar da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da kare Tattalin Arziki kasa (EFCC) daga kai hari gidan tsohon gwamnan jihar Legas, Akinwumi Ambode.

Naija News ta tuno da cewa hukumar EFCC ta afka hari ne a gidan tsohon gwamnan a bisa wata binciken da suke kokarin yi akan gwamnatinsa a baya.

8. Yadda Sojojin Najeriyar ‘suka Taimaka mini da mafita daga tsari – Wadume

Fitaccen dan ta’adda da shugaban barayi a jihar Taraba mai suna Alhaji Hamisu Bala Wadume, wanda aka sake kama ranar Litinin, ya bayyana dalla-dalla game da tserewarsa.

Naija News Hausa ta tuna da cewa a ranar 6 ga watan Agusta da ta gabata, rundunar Sojojin sun hari Jami’an Tsaro sun a yayin da suke kokarin wucewa da Wadume akan hanyar Ibi zuwa Wukari.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNewsHausa