Connect with us

Uncategorized

IMN: ‘Yan Shi’a sun gabatar da ranar Hidimar su duk da Hukuncin Kotu

Published

on

at

Listen to article
00:00 / 00:00

Kungiyar Ci Gaban Harkan Musulunci ta Najeriya ta Kaurace wa Hukuncin Kotu

Duk da sammaci da Kotun Najeriya ta gabatar, Kungiyar Ci gaban Harkar Musulunci a Najeriya (IMN), wacce kuma ake wa lakabi da Shi’a, ta tsayar da ranar Talata don bikinta na Ashura.

Naija News ta fahimci cewa hidimar Ashura wanda kuma ake kira da ranar Ashura, rana ce ta goma ga Muharram, watan farko a kalandar Musulunci.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Babban Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya  (IGP), Mohammed Adamu ya ba da umarni ga dukan rukunin ‘yan sanda a duk jihohin Najeriya da su fara kame shugabannin kungiyar Harkar Musulunci a Najeriya (IMN), da aka fi sani da Shi’a.

IGP Adamu ya bayyana hakan ne bisa umarnin da aka wallafa daga Hedikwatan Rundunar Tsaron zuwa ga dukan Rundunar ‘Yan sanda na Jiha, a ranar 30 ga watan Agusta, 2019, wanda kuwa aka yi gargadi da rashin jinkiri da bin umarnin.