Connect with us

Uncategorized

INEC ta Bayyana Damuwarta kan Rikici gabadin Zaben Jihar Kogi

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Hukumar gudanar da Zaben Kasa, INEC ta jihar Kogi ta nuna damuwar ta game da yiwuwar tashin hankali yayin da zaben gwamnoni na ranar 16 ga Nuwamba na gabatowa.

Naija News ta fahimci cewa Kwamishinan Zabe na mazaba (REC) a Kogi, Farfesa James Apam, a ranar Talata ya bayyana wannan ne a wurin bayyana “fita da jefa kuri’a (GOTV), Ilimin masu jefa ƙuri’a da kuma dakatar da cin zarafin mata a siyasa (STOP VAWIP)” da aka yi a Lokoja, babban birnin jihar Kogi.

Ka tuna da cewa babban dan takaran kujerar Gwamnan Jihar Kogi a karkashin Jam’iyyar Dimokradiyya (PDP), Sanata Dino Melaye ya fadi ga zaben Firamare da Jam’iyyar ta yi a kwanan baya.

Naija News Hausa ta kuma gane da cewa dan takaran ya yi barazana a baya da cewa ya fice Yahaya Bello, Gwamnan Jihar Kogi da ke kan mulki, “a kowace hanya da matsayi” inji Dino Melaye.

Ko da shike bayan da Dino ya fadi ga zaben Firamaren Jam’iyyarsa, PDP ta bashi mukamin jagoran neman takara ga abokin adawan shi ga kujerarshi gwamnan, Musa Wada, wanda ya kasance da nasara ga zaben firamare ta jam’iyyar PDP a Jihar.

KARANTA WANNAN KUMA; Wata Yarinya ta Haska wa Kanta Wuta don Saurayinta ya gaza Biyan Sadakin da aka Yanka Masa