Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Litini, 23 ga Watan Satumba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Litini, 23 ga Watan Satumba, 2019

1. Sojojin Najeriya Sun Kaddamar Da Sabbin Dabarun Yaki da Ta’addanci

Sojojin Najeriya sun ƙaddamar da sabon rukuni mai taken “Operation Positive Identification” a kan ‘yan ta’addar Boko Haram / ISWAP da ke tserewa a yankin Arewa maso Gabashin kasar.

Naija News ta fahimta da cewa an kafa “Operation Positive Identification” ne daga rundunar theater na Operation Lafiya Dole (OPLD).

2. Atiku ya tafi gaban Kotun Koli da sharidu 70 don kalubalantar nasarar Buhari

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Peoples Democratic Pary (PDP), babbar jam’iyyar adawa a Najeriya, a babban zaben da ya gabata, Atiku Abubakar, zai gabatar da kararaki 70 a Kotun Koli kan cin nasarar Shugaba Muhammadu Buhari.

Naija News ta ruwaito tun da farko cewa Kotun daukaka karar zaben shugaban kasa (PEPT) a ranar Laraba, 11 ga Satumbar, ta yi watsi da karar da PDP da dan takarar shugaban kasar suka yi.

3. Shugaba Buhari Ya Bar Najeriya Yau zuwa ga New York

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari a ranar Lahadi, 22 ga Satumba, ya tafi New York, kasar Amurka don halartar taro na 74 na Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA74).

Naija News na da sanin cewa an bude Taro na 74 na Babban Taron Majalisar Dinkin Duniyar (UNGA74) ne a ranar Talata, 17 ga Satumba.

4. An Kashe Mutane Biyu, Wasu kuma da raunuka a yayin harin ‘Yan Bindiga Sun Ji rauni Yayinda Wasu’ Yan bindiga a Adamawa

Wasu ‘yan hari da bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kai hari a wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Numan ta Jihar Adamawa, arewacin Najeriya. Lamarin ya kai ga sanadiyar mutuwar a kalla mutane biyu tare da jikkata wasu da dama, cikinsu har da jami’in soja guda.

A wani rahoto da Naija News ta karba daga jaridar The Nation, an danganta harin ga makiyaya da ke a yankin, mazauna shiyar sun ce maharan sun kewaye garin Shaforon da Kodumti ne da misalin karfe 1:00 na daren Lahadi, tare da harin gidajen mutane.

5. Miyetti Allah sun La’anci Alkalai, ‘Yan Sanda bisa Laifukan da Fulani ke aikatawa

Kungiyar Myetti Allah ta makiyaya (MACBAN), ta zargi alkalai da ‘yan sandan Najeriya kan laifukan da Fulani Makiyaya ke yi a kwanan nan a fadin kasar.

Naija News ta fahimci cewa Mataimakin Shugaban kungiyar MACBAN, Muhammadu Jaure ne ya furta hakan a ranar Asabar, 21 ga Satumba.

6. Tinubu ya Mayar da Martani game da zancen cewa yana goya wa Buhari baya kan tsananta wa Osinbajo

Tsohon gwamnan jihar Legas da kuma jigo a jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Bola Tinubu, ya mayar da martani akan jita-jitar cewa yana marawa shugaba Muhammadu Buhari baya don kokarin makirci ga Yemi Osinbajo, Mataimakin Shugaban Najeriya a kan shugabancin 2023.

Naija News ta fahimci cewa Tinubu ya sanar da hakan ne yayin da yake mayar da martani game da sabbin matakai da Shugaba Muhammadu Buhari ya dauka wanda ake zargin sa da tsananta wa mataimakin nasa ne, in ji rahoton Daily Post.

7. Kungiyar SERAP ta tura ‘sako mai karfi’ ga AGF Malami kan cajin cin amanar Sowore

Kungiyar Kare Hakkokin Tattalin arziki da aiwatar da lissafi (SERAP) ta aikar da wata wasika ga babban Ofisan Shari’ar Tarayya, Abukabar Malami (SAN), tare da gargadin sa da yayi amfani da matsayinsa “ba tare da jinkirta ba ya dauki matakin dakatar da katangewar da aka yi wa jagoran zanga-zangar nuna rashin amincewa ‘RevolutionNow’ watau shugaban jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore, da abokin aikinsa, Olawale Bakare.”

Naija News ta tuna da cewa gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta gabatar da tuhuma bakwai kan Sowore, hare da zargin karkatar da wasu kudade.

8. Gobarar Wuta ta kame Ofishin Ma’aikatar WHO a Osun

A ranar Asabar din da ta gabata, Cibiyar adana rigakafin don kiwon Lafiya ta Duniya (WHO) da ke kasuwar Ayegbaju a Osogbo, babban birnin jihar Osun ta kama da wuta.

Naija News ta fahimci cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar, 21 ga Satumba, sanadiyar wutar lantarki ta Janareto da aka dasa a kusa da cibiyar.

9. CAN tayi kira ga neman a kama Shugaban Miyetti Allah

Kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) ta yi kira da a tsige da kame Shugaban kungiyar Miyetti Allah a cikin gaggawa.

Naija News ta fahimci cewa ƙungiyar kiristocin kasar ta sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa da suka bayar a ranar Lahadi, 22 ga Satumba.

Karanta kari da Cikakkun Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa