Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 24 ga Watan Satumba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Advertisement

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 24 ga Watan Satumba, 2019

1. Kungiyar MASSOB ta fidda bayanai dalla-dalla game da Dalilin da yasa ake Cin Mutuncin Osinbajo

Kungiyar fafutikar kafa kasar Biafra (MASSOB) ta ce rukunin da ke a cikin Aso Rock na tsanantawa da kokarin kunyatar da Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo.

Advertisement
Advertisement

‘Yan Kungiyar Biafra din sun kuma zargi shugaban kasa Muhammadu Buhari da rashin jinkirta ko nuna damuwa domin kare Mataimakin Shugaban kasar.

Advertisement
2. A karshe, Shugabannin Tsaro Sun Bayyana A gaban Gidan Majalisu

Wakilan Majalisar Wakilai sun gana da Shugabannin Ma’aikata domin tattaunawa kan yadda ya za magance matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya.

Advertisement
Advertisement

Ko da shike Babban Hafsan Sojoji, Laftanar-Janar Tukur Buratai da Sufeto Janar na ‘yan sanda, Mohammed Adamu ba su halarci taron da aka yi na kofa kulle ba.

Advertisement
3. Alkali Ngwuta da aka ‘Dakatar ya sake komawa ga aiki a Kotun Koli

Mai shari’a, Sylvester Ngwuta wanda aka dakatar da shi daga benci na Kotun Koli ranar Litinin ya dawo da ci gaba da aikinsa.

Advertisement

Naija News ta tuno da cewa Ma’aikatan Tsaro ta Jiha da Jiha (DSS) a watan Agustan 2016 sun fada gidan Ngwuta da wasu alƙalai da bincike.

Advertisement
Advertisement
4. Kotun ta Tabbatar da nasarar Sanwo-Olu kan zaben Jihar Legas

Kotun daukaka kara a Legas, ta soke karar da Jam’iyyar Labour (LP) ta gabatar wa Mista Babajide Sanwo-Olu a kan zababben gwamnan jihar Legas a zaben 9 ga watan Maris da ta gabata.

Advertisement

Kotun ta ayyana karar a zaman “aikin banza ne kuma mara amfani”, kotun ta ce masu karar (LP da Ifagbemi Awamaridi, dan takarar gwamna a zaben) sun gaza gabatar da shaidar rashin cancantar kwakwalwa da aka gurfanar da Sanwo-Olu.

Advertisement
5. Gwamna El-Rufai Ya Sanya Yaron sa a Makarantar Firamaren gwamnati

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir-El-Rufai ya jefa dan nasa, Abubakar Al-Siddique El-Rufai a makarantar firamare ta gwamnati a jihar.

Advertisement
Advertisement

Bisa rahoton da Naija News ta tattara, Gwamnan ya sanya Al-Siddique ne a dan Aji na Farko a Firamare ga makarantar Kaduna Capital School ranar Litinin.

Advertisement
6. Malami da Emefiele sun jagoranci Wakilan Najeriya Zuwa Ingila don Gwagwarmaya da zancen P&ID

Wakilan gwamnatin tarayya da suka hada da gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele, da kuma babban lauyan hukumar (AGF), Abubakar Malami, sun rigaya sun kasance a Burtaniya don kubutar da Najeriya daga wata zargi babban Bashi ga Hukumar Masana’anta ta (P&ID).

Advertisement

Wakilan da suka bar Najeriya a ranar Asabar din da ta gabata sun hada da sufeto-janar na ‘yan sanda (Adamu IGP) Mohammed Adamu; mukaddashin shugaban hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC), Ibrahim Magu da kuma ministan yada labarai, Lai Mohammed.

Advertisement
Advertisement
7. Mai Yiwuwa Kudu Maso Gabashin Kasar ta Rungumi IPOB A shekara ta 2023 – inji Ezeife

Chukwuemeka Ezeife, tsohon gwamnan jihar Anambra, ya bayyana da cewa mai yiwuwa tsofaffi a Kudu maso Gabas na kasar Najeriya su rungumi Nnamdi Kanu, jagoran kungiyar ‘Yan asalin yankin Biafra (IPOB) a shekarar 2023.

Advertisement

Naija News ta fahimci cewa tsohon Gwamnan ya ce ba mamaki su tilastawa a yankin kasar da mara wa kungiyar IPOB baya idan har sauran sassan Najeriya suka kulla sheri na kokarin hana yankin su da Shugabancin a 2023.

Advertisement
8. 2023: Fasto Tunde Bakare Ya Bayyana Wanda Zai Karɓi Shugabanci daga Buhari a gaba

Babban Fasto da Jagoran Ikilisiyar ‘The Latter Rain Assembly’ a jihar Legas, Fasto Tunde Bakare ya baiyana da cewa shi zai zama Shugaban Najeriya a 2023.

Advertisement
Advertisement

Babban Malami da Faston ya baiyana da cewa zai karbi mulki daga hannun Shugaba Muhammadu Buhari lokacin da wa’adinsa ya kare a shekarar 2023.

Advertisement
Advertisement

Ka samu kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa

Advertisement