Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 22 ga Watan Oktoba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 22 ga Watan Oktoba, 2019

1. #RevolutionNow: Kotu ta rage Kudin Belin Sowore zuwa Naira miliyan 50

Mai shari’a Ijeoma na Babbar Kotun Tarayya da ke zaune a Abuja ta duba yanayin belin da ya shafi Omoyele Sowore da Hukumar DSS.

A yayin da take bayani a ranar Litinin, lokacin da mai gabatar da kara na zanga-zangar #RevolutionNow, Omoyele Sowore, ke neman sassauci kan yanayin belin sa, Mai shari’a Ijeoma ta ce za a iya rage belin Sowore ne zuwa miliyan 50 kawai, shi kuma Bakare zuwa miliyan N20.

2. Ngige Ya Bayyana Lokacinda Biyan mafi karancin albashi Zai Samu Tasiri

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce cikakken aiwatarwa da kuma biyan sabon mafi karancin albashi zai gudana ba da jinkirta ba.

Naija News ta fahimci cewa Ministan kwadago da aiki, Chris Ngige ne ya sanar da hakan yayin da yake zantawa da manema labarai kwanan nan a birnin tarayya, Abuja.

3. Benue: Gwamna Ortom Ya Gargadi Buhari Kan Makiyaya daga kasar Waje

Gwamna Samuel Ortom, Gwamnan jihar Benue ya bukaci gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da ya nemi hanyoyin hana makiyayan kasashen waje shiga Najeriya ba bisa ka’ida ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai wa Malama Wanhena Cheku ziyara, wacce makiyaya zuwa yiwa raunana a kwanakin baya da ake bawa kulawa a Asibitin Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Apir a Makurdi.

4. Kotu ta Ba da hukunci akan Gidan Saraki da ke a Ikoyi

Babbar Kotun Tarayya da ke zaune a Legas ta ba da umarnin amshe Mallaka biyu a Ikoyi wacce ke da liki da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki.

Mai shari’a Mohammed Liman ya ba da wannan hukuncin ne biyo bayan wani kara da Hukumar Yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC) ta gabatar.

5. Wanda ake zargi da Kisa, David West, zai bayyana a gaban kotu

Za a gurfanar da Gracious David West, wanda ake zargi da kisan gilla, a gaban babbar kotun jihar Ribas.

Ka tuna cewa wasu mutane da dama a jihar sun tada murya da kai tsaye kan kashe-kashen mata da ake yi Otal.

6. An rantsar da Edward Onoja a Matsayin Mataimakin Gwamnan Kogi

Anyi hidimar rantsar da Cif Edward Onoja, a ranar Litinin, 21 ga Oktoba 2019 a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kogi.

Naija News ta ba da rahoton cewa ‘yan majalisar sun tantance sabon Mataimakin gwamnan wanda daga nan suka neme shi da maye gurbin tsohon mataimakin gwamnan jihar, Mista Simon Achuba.

7. Bankin duniya ta amince da bada rancen dala biliyan uku ga Najeriya

Babban bankin duniya ta amince da bukatar dala biliyan 3 da Najeriya ta nema don fadada hanyoyin rarrabar da kayan wutar lantarki a kasar.

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, da take magana bayan amincewar wannan rancen a yayin taron bankin duniya, ta ce za a rabar da rancen ne a kashi hudu na dala miliyan 750 kowanne daga shekara mai zuwa.

8. 2023: Yadda Tinubu zai Iya samun kuri’u 20m Daga Kudu maso Yamma – Ogunlewe

Wani tsohon Ministan ayyuka, Sanata Adeseye Ogunlewe, ya ba da sanarwar cewa Asiwaju Bola Tinubu, zai iya samun yawar kuri’u miliyan 20 daga Kudu maso Yamma shi kadai idan har ya yanke shawara ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2023.

Ogunlewe a cikin karyewar alkalummansa ya ce, Tinubu na iya samun kuri’u miliyan 5 daga jihar Legas shi kadai idan ‘yan siyasa daga yankin sun sanya himma a hidimar.

Ka samu kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa