Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 29 ga Watan Oktoba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Advertisement

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 29 ga Watan Oktoba, 2019

1. Kotun Koli ta yanke hukuncin Karshe kan Karar HDP game da zaben Buhari

Kotun kolin Najeriya ta yi watsi da wata sabuwar kara da kungiyar Hope Democratic Party (HDP) da dan takarar shugaban kasa, Ambrose Owuru, suka yi a kan nasarar Shugaba Muhammadu Buhari a zaben shugaban kasa da aka yi a ranar 23 ga Fabrairu 2019.

Advertisement
Advertisement

Naija News Hausa na tunatar da cewa HDP da dan takarar shugaban kasarsu a zaben 2019 sun nemi kotun kolin ta sauya kanta a hukuncin da aka yanke ranar 3 ga Oktoba.

Advertisement
2. Gwamnonin Jihohi Sun Dauki Sabuwar Mataki Kan Mafi Karancin Albashi

Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF), ta ce sakamakon karin yawaitar Dokar mafi karancin albashi na N30,000 zai dogara ne da karfin kowace Jiha a kasar.

Advertisement
Advertisement

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta bayar da rahoton cewa, Kayode Fayemi, shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Ekiti ya bayyana hakan yayin da yake yiwa manema labarai karin haske a karshen taron da aka gudanar a Abuja ranar Litinin.

Advertisement
3. Shugaba Buhari ya tattauna batun sake bude Bodar kasar a taron Siiri da Gwamna Emefiele

Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya gana a ranar Litini da Godwin Emefiele, gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) a wani taron siiri.

Advertisement

Taron wanda ya gudana a ofishin Shugaban kasa nan cikin Fadar Shugaban kasa, Aso Villa, ya fara ne da misalin karfe 11:30 na safiyar ranar Litini.

Advertisement
Advertisement
4. ‘Yan Hari da Bindiga sun Sace Insfekta na ‘Yan Sanda, tare da Wasu A Abuja

An samu rahoton cewa an sace Insfekta Janar na ‘yan sandan Najeriya (NPF) da wani mutum guda, a kauyen Rubochi da ke Kuje, karamar hukuma a Birnin Tarayyar Najeriya (FCT), Abuja.

Advertisement

Rahoton da aka bayar akan jaridar The Nation wanda jaridar ta Naija News ta gane da ita ya bayyana da cewa an sace Sufeto Janar na ‘Yan Sandar ne da wani mutum a tsakar dare ranar Lahadi, 27 ga Oktoba ta hannun wasu ‘yan hari da bindiga wadanda suka afka wa al’ummar yankin da harbe-harbe.

Advertisement
5. Atiku vs Buhari: Jam’iyyar APC ta Bayyana wata makircin da PDP ke gudanarwa game da Kotun Koli

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta zargi jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da shirin yin amfani da kafafen yada labarai na kasar waje don dakile masu shari’ar Najeriya.

Advertisement
Advertisement

Naija News ta fahimta da cewa Kotun Koli ta bayar da ranar Laraba, 30 ga Oktoba, don yanke hukunci kan karar da PDP da dan takarar shugabanta, Atiku Abubakar, suka yi game da hukuncin Kotun daukaka kara ta Shugaban Kasa (PEPT).

Advertisement
6. IPPIS: Babu biya, Babu Aiki – ASUU ta Kalubalanci Gwamnatin Tarayya

Kungiyar Malaman Manyan Jami’o’i (ASUU) ta yi barazanar cewa za ta yi watsi da yin aiki saboda shirin da Gwamnatin Tarayya ta yi na yi wa ma’aikatan jami’ar rajista a cikin Tsarin Hadin Albashi da na Ma’aikata (IPPIS).

Advertisement

Kungiyar ta sanar da matsayin nata ne a ranar Lahadin da ta gabata yayin wani taron manema labarai da ta gudanar a Jami’ar Ibadan ta reshen Kudu maso yamma.

Advertisement
Advertisement
7. An kashe wani dan Najeriya, Da kuma yiwa wasu 2 jikkata a wani harin Xenophoic a kasar South Afrika

An kashe wani dan Najeriya, Chikamso Ufordi, dan yankin karamar hukumar Awgu ta jihar Enugu da ke kudu maso gabashin Najeriya a wani sabon hari na ‘yan kunar bakin wake a kasar South Afirka.

Advertisement

Naija News ta fahimta da cewa wani sabon tashin hankali wanda ya dauke rayuwar Ufordi, ta faru ne da misalin karfe

Advertisement

7 ta maraicen ranar Asabar da ta gabata a Nigel.

Advertisement
Advertisement
8. Shugaba Buhari Zai kai Ziyarar Kai Tsaye zuwa Landan

Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya bar kasar a ranar Litinin a wata ziyarar aiki da zai yi zuwa Masarautar Saudi Arabiya don halartar Babban Taron Hadin gwiwar Kawo Zuba Jari (FII) a Riyadh.

Advertisement

Kamar yadda labarai na Naija News ta ruwaito, Shugaba Buhari zai yi tattaunawa da Mai Girma Sarki Salman da Mai Girma Sarki Abdullah ll na Jordan a yayin taron.

Advertisement
9. 2023: Shehu Sani Ya Bayyana zabin sa ga Shugabancin Kasar Najeriya a zabe ta gaba

Tsohon sanata mai wakilcir Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani ya ba da sanarwar sauya shugabancin kasa zuwa yankin Kudancin kasar nan a 2023.

Advertisement
Advertisement

Sani ya yi nuni da cewa rashin ba wasu yankuna a kasar damar shugabancin kasa a 2023 na iya haifar da karin rikici a siyasan da kuma kawo habaka a Najeriya.

Advertisement
Advertisement

Ka samu Kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa

Advertisement