Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Jumma’a, 1 ga Watan Nuwamba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Advertisement

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Jumma’a, 1 ga Watan Nuwamba, 2019

1. Shugaba Buhari Ya Isa Makka Don Umrah

Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari wanda ya tafi kasar Saudi Arabiya ranar Litinin ya isa Makka a ranar alhamis a karshen Taron kwanaki uku na zuba jari a a kasa wanda ya gudana a Riyadh.

Advertisement
Advertisement

Shugaba Buhari ya karbi marbata ne daga hannun Yariman Sarki Bader bin Sultan bin Abdulaziz, Mataimakin Gwamna na Yankin Makka da sauran jami’an gwamnati a filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz, Jeddah, da misalin karfe 7.05 ta maraice a lokacin gida.

Advertisement
2. Shugaba Buhari bai kai Obasanjo Zuwa Kasar Waje ba  – Inji Oshiomhole

Ciyaman tarayyar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a hidimar neman zabe, Adams Oshiomhole, ya ayyana da cewa Cif Olusegun Obasanjo ya yi tafiya fiye da Shugaba Muhammadu Buhari a lokacin da yake shugabancin Najeriya.

Advertisement
Advertisement

Oshiomhole ya gabatar da wannan furcin ne a yayin da yake kokarin kare yawon shakatawa da yawa na Shugaba Buhari tun lokacin da aka zaɓe shi a matsayin shugaban Najeriya a shekarar 2015.

Advertisement
3. EFCC ta gayyaci ‘Yan Kasuwa na kasashen waje don su Sayi Mallakar Diezani ta Biliyan N14.4bn

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da kare Tattalin Arzikin Kasa (EFCC) ta tuntuɓi ‘yan kasuwa na ƙasan waje don sayan kayan ado mai tsadar dala miliyan 40 (kusan Naira biliyan 14 a kudin Najeriya), waɗanda aka karɓa daga tsohuwar Ministan Albarkatun Man Fetur, Diezani Alison-Madueke.

Advertisement

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta bayar da rahoton cewa mukaddashin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Ibrahim Magu ne ya bayyana hakan.

Advertisement
Advertisement
4. Biafra: Nnamdi Kanu Ya Bada Sharadin Da Zai Dawo da Shi A Najeriya

Shugaban kungiyar ‘Yan asalin yankin Biafra (IPOB), Mazi Nnamdi Kanu ya ba da sharadin dawowarsa Najeriya don ci gaba da fuskantar shari’a.

Advertisement

Shugaban kungiyar IPOB ya ce a shirye yake ya dawo kasar ya fuskanci shari’a idan har kotu ta iya ba da tabbacin lafiyarsa.

Advertisement
5. Shugaban Jam’iyyar APC yayi Magana kan Tsarin Shugabanci

Ciyaman Tarayyar Jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Adams Oshiomhole, yayi alwashin ba zai amsa a bainar jama’a ba game da zarge-zargen da Farfesa Itse Sagay ya yi masa.

Advertisement
Advertisement

Naija News ta tuno da cewa Sagay, Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa kan yaki da cin hanci da rashawa (PACAC), ya ce tsaurin ra’ayi da tsarin Oshiomhole zai sa jam’iyyar ta rasa iko a wasu jihohin kasar.

Advertisement
6. Gwamnatin Tarayya Ta Dage Kuntatawa ga Wasu Kamfanoni Masu Zaman Kansu Guda biyu a arewa maso gabas

Gwamnatin Tarayyar Najeriya a jagorancin Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta amince da sauya dakatarwar da aka sanya kan kungiyoyi biyu na agaji na kasa da kasa (kungiyoyi masu zaman kansu) a Arewa maso Gabas.

Advertisement

Naija News ta tuno da cewa, rundunar ‘Operation Lafiya Dole” ta rundunar sojojin Najeriya ta dakatar da wadannan kungiyoyi masu zaman kansu guda biyu, a ranar 19 ga Satumbar da 24 ga Satumbar, a bisa zargin cewa suna wadatar da abinci da magunguna ga maharan Boko Haram.

Advertisement
Advertisement
7. Zaben Kogi: INEC ta bayyana Abin da Zai Faru da Yahaya Bello Akan Rijista Biyu

Hukumar Gudanar Da Zaben Kasa (INEC) ta bayyana matsayinta kan tuhume-tuhumen yin rijistar mutum biyu da aka yi wa Gwamna Yahaya Bello na Jihar Kogi.

Advertisement

Naija News ta tuno da cewa Natasha Akpoti, memba a cikin jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), ta nemi wata babbar kotun tarayya da ke Abuja da ta tsige gwamnan daga sake neman takara a jihar Kogi game da batun rajistar ninki biyu a matsayin mai jefa kuri’a.

Advertisement
8. Mazauna Sun Guje A Yayin da Wata Motar Tanki ta Fadi A Onitsha

Wata mummunar bala’i ta afku a ranar Alhamis bayan da wata motar tanki da ke dauke da man fetur ta rutsa cikin wata rami a kan titin Onitsha / Enugu ta tashar Chipex, da ke Onitsha.

Advertisement
Advertisement

Ko da shika a lokacin da aka wallafa wannan rahoto, ba a samu barkewar gobara ba daga faduwar motar, amma wata majiya ta ce mazauna kusa da yankin suna tserewa daga wurin saboda fargabar barkewar wutar.

Advertisement
Advertisement

Ka samu Kari da Cikakken Labaran Najeriya ta Yau a Naija News Hausa

Advertisement