Connect with us

Uncategorized

An Kame Wani Mutumi Mai Shekaru 42 A Yayin Sayar da Dansa a Jihar Nasarawa

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Naija News Hausa ta karbi rahoron kame wani mutum mai shekaru 42 da haihuwa da aka yi, wanda aka zargeshi da kokarin sayar da dansa mai shekara uku da haifuwa a Lafia, babban birnin jihar Nasarawa kan yawar kudi miliyan N5.

Kwamandan rundunar tsaro ta farin kaya ta Najeriya (NSCDC) wadda aka fi sani da suna ‘Civil Defence’ Mista Mohammed Mahmoud-Fari ya bayyanawa manema labarai da cewa, sun kama wanda ake zargin ne a wani samamen da jami’an rundunar suka yi bayan da suka karbi wata likin bayanai game da niyyar siyarwa daga wani mazauni.

A bayanin Mahmoud, ya bayyana da cewa;

“Jami’an mu sun karbi rahoton matakin da mahaifin yaron ya dauka a sirance, suka kuwa fara tattaunawa da shi a matsayin zasu sayi yaron daga hannunsa, inda ya bayyana masu da cewa zai sayar da shi a kan kudi Naira miliyan biyar.”

“Ya nuna da cewa yana son ya karbi kudin ne a warware cikin jikka, ana cikin hirar hakan ne muka kuwa kama shi a garin Lafiya,” in ji Mahmoud-Fari.

Mahmoud ya bayyana cewa mutumin da aka kama da zargin sayar da dansa mazuni ne a karamar hukumar Obi, yana kuwa da mata biyar da ‘ya’ya 23, wadanda a cikinsu ya riga ya sayar da diya guda tun a baya.

Ya kara da cewa wanda ake zargin ya amsa da amince da laifinsa kuma, ya danganta matakin da ya dauka akan yanayin wahalar tallauci da ake fuskanta a kasar, a kuma cewa ya sayar da dan nasa ne domin ya samu kudin da zai kula da sauran diyansa da matansa biyar.

KARANTA WANNAN KUMA; Cututtuka da Namijin Goro ke Iya Warkas wa a jikin Dan Adam.