Connect with us

Uncategorized

APC/PDP: An Bada Hutun Aiki ga Al’ummar Jihar Kogi don Zaben Ranar Asabar

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Gwamnatin Jihar Kogi ta bayar da hutu ga mai’aika, ‘yan makaranta da al’umar jihar domin hidimar zaben tseren kujerar gwamna da za a yi a jihar a ranar Asabar, 16 ga watan Nuwamba 2019.

Gwamna Yahaya Bello ya amince da ranar juma’a, 15 ga Nuwamba a matsayin ranar hutu ta jama’a da dukkanin makarantun da ke jihar.

A wata sanarwa da Sakataren dindindin na ma’aikatar ilimi na jihar, Mista Eric Aina ya sanya wa hannu, ya ce dukan makarantun gwamnati da masu zaman kansu za su ci gaba da hutu daga ranar 15 ga Nuwamba, 2019, gabadin zaben ranar 16 ga Nuwamba da zai gudana a jihar.

Gabatar da hutun ya kunshi ganin tabbatar da cewa dukkan dalibai sun hade da danginsu yayin hidimar zaben jihar da ya gabato.

Naija News ta samu fahimtar cewa hutun zai kawo karshe ne a ranar Litini, 18 ga Nuwamba, 2019 a yayin da makarantu zasu ci gaba da ayukansu.

Ka tuna a wata faifan bidiyo wadda kamfanin dilancin labarai ta Naija News Hausa rabas kamar yadda ta gano a layin sada zumunta ya nuna lokacin mutanen Kogi suka kunyatar da Gwamna jihar Kogi, Yahaya Bell a garin Lokoja, babban birnin Jihar.

Abin ya faru ne da gwamnan a yammacin ranar Lahadi, 10 ga Nuwamba a Lokoja, babban birnin jihar Kogi a yayin yawon neman zaben da Bello yayi a jihar.

A cikin faifan bidiyon wanda aka rabas ta shafin yanar gizon Twitter a hannun Sanata Dino Melaye, yayi nunin yadda mutanen Lokoja suka yiwa gwamna tsuwa da zage-zage a lokacin da ayarin motocin sa suke wucewa ta hanyar Lokoja.