Connect with us

Labaran Najeriya

Buhari: Matasan Arewa Sun Nemi Osinbajo da Ya Yaki Shugabancin Kasar Ko kuma ya yi Murabus da Matsayinsa

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kungiyar Arewa Youth Consultative Forum ta tuhumi Mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo, da mayar da harin tsanancin da fadar shugaban kasar ke yi masa.

Babban Shugaban Kungiyar Matasan Arewa (AYCF), Yerima Shettima, a wata hira da jaridar Daily Post, ya lura cewa za a kori Osinbajo idan ya ki mayar da harin tsanantawa da wulakanci da ake masa, ko kuma ya yi murabus cikin mutunci da matsayinsa.

Shettima ya fadi hakan ne a yayin mayar da martani kan wasu sabin harin tsanantawa da kunyatarwa da mataimakin shugaban kasar ke fuskanta a fadar shugabancin kasa.

Shugana AYCF din ya nace a bayaninsa da cewa gwamnatin kasar a jagorancin Muhammadu Buhari tana tsanantawa Osinbajo, ya na kuwa mamakin abin da ya sa Mataimakin Shugaban kasar ya yi shuru game da rikicin da ke gudana da shi a Shugabancin.

“Mun gane da cewa wasu mutane a ofisoshin shugabancin kasar suna yin amfani da tsarin jagorancin ne don biyan bukatun kansu, Ko kun yarda ko kuma ku ki amincewa, akwai wani ko wasu da ke neman tabbatar da cewa an cire Mataimakin Shugaban kasa a tsarin mulkin don neman hanyarsa ta zuwa shugabancin kasar a 2023.” Inji Shettima.

“Abu daya nike bukatan ku gane a wannan gwamnatin, ko ta yaya suka ki amince da wannan zargin, tabbas akwai abin da ke gudana a boye. A daidai lokacin da suka ce Shugaban kasar da Mataimakinsa suna cikin kyakkyawan yanayi Na san wani abu da ba daidai ba na gudana, saboda ba a taba hayaki ba ba tare da wuta ba.”

“Maimakon a kori mataimakan Mataimakin Shugaban kasar, me zai hana a dubi Majalisar Dokoki ta kasa, idan da da gaske ake da son a rage kashe-kashen kudi a shugabanci a Najeriya me zai hana a nemi tsige wasu ma’aikata da ke a majalisar da basu da wata aiki na fari ko baka da suke yi, amma sai karban albashin da bai da ma’ana. Ko kuma a rage adadin yawar ‘yan majalisar, maimakon duba ofishin Mataimakin Shugaban.”

“Wasu daga cikin mu sun san cewa an zazzage fagen fama. Tabbas ana matukar raunana Osinbajo, wannan ya nuna a fili cewa ana hari da kuma neman a tsige shi ne daga tsarin mulkin. Na yi mamakin yadda bai fito ba da karfin gwiwa don neman tausayi da goyon bayan ‘yan Najeriya ya kuma bayyana zuciyarsa. Yana zaune kawai a cikin nutsuwa saboda yana son tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa shi mutumin Allah ne. Batun siyasa ba batun Allah bane, ya shafi batutuwa da yawa, tilas ne a nuna kwaraewa da iya taka rawa. Na san shi Farfesa ne na shari’a amma akwai bukatar ya fito ya fadawa ‘yan Najeriya abin da ke faruwa, idan ya ci gaba da yin shiru, kawai zai farka ne a wata safiya ya ga cewa an cire shi. “

Ka tuna a baya kamar yadda Naija News Hausa ta sanar, da cewa Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Femi Fani-Kayode ya yi zargin Shugaba Muhammadu Buhari da wulakantar da Mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo a hanyoyi goma.