Connect with us

Uncategorized

Bazaka taba zama Shugaban Kasar Najeriya ba – Bishop ya fadawa El-Rufai

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Bishop na Zariya Diocese (Anglican Communion), Rt Rev Abiodun Ogunyemi ya yi ikirarin cewa gwamna Nasir el-Rufai na jihar Kaduna ba zai taba ci nasara ga fito takarar shugabancin Najeriya ba.

Bishop din ya bayyana cewa ya fadi hakan ne da yi imanin cewa gwamnan jihar Kaduna ya shirya domin takara a 2023.

Naija News ta fahimta da cewa Ogunyemi ya yi wannan ikirarin ne yayin da yake mayar da martani ga shirin da gwamnan yayi a kwanakin da suka gabata na rushe gidan St George Cathedral mai tsawon shekaru 110 da aka gina, wanda ke a Sabon-Gari Zariya da kuma wani shirin da ake zargi na rushe kadarorin Cocin da ke a Sabon gari.

Bishop din a shafin intanet na Iklisiyar ya la’anta Bishop din Wusasa Diocese, lardin Anglican na Kaduna, Rev. Ali Buba Lamido, wanda ya yaba wa gwamna el-Rufai, a ranar Litinin kan shawarar da ya yanke na rushe cocin.

Ya ce duk wani yunƙuri na rushe ko tsananta wa duk wata Majami’a a jihar Kaduna laifi ne ga Allah da kuma Kiristoci a duk faɗin ƙasar.

“KASUPDA ta rubuta wasika kan umarnin gwamna El-Rufai a gare mu da mu bar harabar majami’ar a cikin kwanaki bakwai, mun kuwa ba da amsa ta hanyoyin da suka fi dacewa tare da kungiyar CAN da sauran kungiyoyin kirista a duk faɗin duniya.”

“Mai makon mu nemi afuwa daga gwamnan, ya dace gwamna ya nemi afuwa daga Ikilisiyar da ma sauran jama’a saboda kunyata kanshi da yake yi da irin wannan umarni da yake gabatarwa.”

Ya bukaci Gwamnan jihar Kaduna da ya daina kunyatar da kansa tare da rushe majami’u a kowane bangare na jihar Kaduna.