Connect with us

Uncategorized

Da Lai Mohammed Ya Mutu ko Idan Da A Ce an Kafa Dokar Kisa kan Kalamun Kiyayya tun Wa’adin Jonathan – Abaribe Ya Gayawa Lai Mohammed

Published

on

at

Advertisement

Sanata Enyinnaya Abaribe ya mayar da martani game da dokar mutuwa ta hanyar rataye wanda ke a kunshe cikin wata sabuwar tsarin da Majalisar Dattawa ke kokarin kafawa.

Advertisement
Advertisement

Ka tuna kamar yadda Naija News Hausa ta ruwaito a baya cewa Jam’iyyar PDP Sun Yi Allah Wadai da Dokar Kisa ga Masu Yada kalaman Kiyayya da Majalisar ta Shirya da kafawa.

Advertisement

Abaribe a cikin yada yawunsa ya haɗu da wasu ‘yan Najeriyar don ƙin amincewa da dokar.

Advertisement
Advertisement

Yace; Idan da an riga an zartar da irin wannan dokar a lokacin mulkin tsohon Shugaba Goodluck Jonathan, da Ministan Yada Labarai da Al’adu, Lai Mohammed a yanzu ya mutu ko.

Advertisement

Abaribe ya ce Lai Mohammed ya furta kalamai masu yawa da ba za a iya bayyanawa ba kan Jonathan a lokacin wa’adinsa, ya kara da cewa ba a hanna shi hakkinsa na bayyana ra’ayin nasa ba a lokacin.

Advertisement

A lokacin da aka nemi Abaribe da bayani game da batun dokar a gidan talabijin na TV Channels, Sanatan ya amsa da cewa:

Advertisement
Advertisement

“Ku bari in tunar da ku da karanta muku wasu zance domin bada karin haske a wannan zancen.”

Advertisement

“Bai kamata a yi dauriya da gwamnatin da ba ta shirye don daukar nauyin al’ummar ta ba. Gwamnati kasa ke da hakin kare ‘yan kasarta amma ba kafa baki ba ga neman zargi. Yanzu, wannan Shugaban yariga ya bayyana a fili a tsarin sa ga duniya da cewa ya kasa ga shugabanci. A cikin tarihin shugabanci, ba a taba samun gwamnati marasa manufa da hanayar ci gaba ba kamar irin wannan gwamnatin. Wannan gwamnatin tana tafiyar da ƙasar gabaɗaya tare da hadin shugabannai marasa himma da kuma cikke da cin hanci da rashawa. Hakikan wannan gwamnatin bata da wata alaka da kabilanci, amma kawai cikke da shugabannai da basu cancanta ba ga tsarin mulki.”

Advertisement

Waɗannan sune kalmomin Lai Mohammed, Ministan Labarai tsakanin shekarar 2012 da 2014.

Advertisement
Advertisement

Ina tabbatar maku da cewa a yau duk wanda ya faɗi irin wannan kalamai da an riga an dakile shi da zargin kalamun kiyayya da bacin shugabancin kasa.

Advertisement

Zasu ce ka baci shugaban kasa da kuma raina shi, a hakan kuma a daure ka da jefa ka a kurkuku. Idan da ace an riga an kafa dokar kisa ta hanyar ratayewa ga masu kalaman kiyayya tun a wa’adin jonathan, shin da Lai Mohammed da wadannan kalaman da ya furta, kuna ganin da zai saura da rai a yau?

Advertisement

Wannan shirin ba komai bane illa rashin juriya da kuma neman tsananta wa rayuwa al’umar kasa. Mutumin da ya furta irin wadannan kalamu a baya sai ga shi a yau da kafa dokar da zai hana wasu da yin hakan.

Advertisement
Advertisement
Advertisement

“Ya dace kowane dan Najeriya ya farka daga barci, ya kuma gane da cewa wannan gwamnatin bata da kirki ko wata manufa ta kwarai ga al’ummarta” inji Abaribe.

Advertisement