Connect with us

Uncategorized

‘Yan Fashi da Makami sun Tari Motar ‘Yan Sanda a Kaduna

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wasu da ake zargin su da zama ‘yan fashi da makami sun kaiwa motar ‘yan sanda hari da aska masa wuta a cikin garin Kaduna

Lamarin ya faru ne a dajin Kwanar Labi-Kwaru, kusa da kauyen Udawa a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

Wata majiya da ba ta bada rahoton da kuma aka hana bayyana sunan ta, ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 11 na dare bayan wata musayar harbin bindiga da ya afku tsakanin ‘yan sanda tare da wasu da ake zarginsu da zaman ‘yan fashi, a yayin da ‘yan sandan ke akan hanyarsu ta zuwa Kaduna daga Birnin Gwari.

Naija News Hausa ta tuna da cewa ‘yan fashi sun saba da tarin mutane a kan babban hanyar ta Birnin Gwari zuwa Kaduna, inda suke tsananta da kwace mallakar mutane a kan hanayar.

Wata majiya a cikin ‘yan banga da ke tsaro akan hanyoyin sun shaida wa manema labarai da cewa wani dan sanda ya ji rauni a yayin harin, yayin da wasu kuma suka tsere wa rayuwarsu zuwa cikin dajin.

“Su ‘yan sanda na kan tafiya ne a cikin wata farin mota a wani wurin da ake kira Kwaru bayan Kwanar Labi kusa da garin Udawa a lokacin da aka hare su. ‘Yan fashin sun kasance ne da yawarsu, a yayin da suka yi wa dan sanda ɗaya raunuka yayin da sauran suka tsere zuwa daji” inji Majiyar.

“Ko da shike babu wani rai da aka rasa a cikin harin amma ‘yan bindigar sun banka wa motar ‘yan sandan wuta,” in ji shi.

“Na ga lokacin da motar ke konewa saboda ina kan tafiya a wannan ranar a amma dai mun kasa da iya tsayawa ba saboda yankin da lamarin ya faru an wuri ne mai hadari sosai,” in ji shi wani mazaunin yankin da ya ki bayar da sunansa.

Ko da shike a yayin karban rahoton da aka tuntubi Ofisan Hurda da Jama’a na Rundunar Tsaron jihar, ASP Sulaiman Abubakar, ya fada da cewa zai samu cikakken bayani game da harin, a bayan hakan kuma zai bayar da rahoto ga manema labarai, amma dai hakan bai samu ba a lokacin da aka wallafa wannan rahoton.