Connect with us

Labaran Najeriya

Bayanin Shugaba Buhari Game da Zaben Gwamnoni a Jihar Kogi da Bayelsa

Published

on

at

Advertisement

A ranar Alhamis din da ta gabata ne Shugaba Muhammadu Buhari ya ba da tabbacin cewa za a ba masu jefa kuri’a damar yanke hukunci a kan shugabanninsu a zaben Gwamnonin jihohin Bayelsa da Kogi.

Advertisement
Advertisement

Naija News ta rahoto da cewa Hukumar Gudanar da Hidimar Zaben Kasa (INEC) ta sanya ranar Asabar, 16 ga Nuwamba, 2019 don gudanar da zaben jihar Bayelsa da ta Kogi.

Advertisement

A wata sanarwa da mai taimaka ma shugaban a kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ya bayar, Buhari ya yi kira da a yi adalci da nuna gaskiya a yayin zabukan.

Advertisement
Advertisement

Shugaban ya kuma tuhumi hukumomin tsaro da su kasance da bin ka’ida da kuma kada su nuna banbacewa a yayin zaben a jihohin biyu.

Advertisement

Ya kuma bukaci al’umma masu jefa kuri’u a Bayelsa da Kogi da su yi amfani da damar su a cikin kwanciyar hankali da tsari don zaben shugabannansu.

Advertisement

Bayaninsa na kamar haka;

Advertisement
Advertisement

“A ranar Asabar, 16 ga Nuwamba, za a bar masu jefa kuri’a a jihohi biyun, Bayelsa da Kogi don su yanke hukunci da kansu ta hanyar zabe akan wanda zai karbi ragamar shugabancin jihohinsu na shekaru hudu masu zuwa.

Advertisement
Advertisement

Na bukaci al’umma masu jefa kuri’u a Bayelsa da Kogi da su yi amfani da damar su a cikin kwanciyar hankali da tsari don zaben shugabannansu.”

Advertisement