Connect with us

Uncategorized

APC: Hukumar INEC ta Gabatar da Mai Nasara ga Zaben Jihar Bayelsa (Kalli Yawar Kuri’u da ya kai shi ga Nasara)

Published

on

at

Advertisement

INEC ta ayyana David Lyon na dan takarar APC a zaben Bayelsa

Hukumar da ke gudanar da hidimar zabe ta Kasa (INEC), ta ayyana David Lyon, dan takara daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC),  jam’iyyar da ke mulkin Najeriya, a matsayin wanda ya yi nasara da lashe zaben Gwamnonin Bayelsa.

Advertisement
Advertisement

Naija News ta samu tabbacin rahoton nasarar Lyon ne a matsayin wanda ya lashe zaben Bayelsa ta hannun shugaba da jagoran hidimar zaben jihar, Mataimakin shugaban jami’ar Benin, Farfesa Faraday Orunmuwese, a safiyar Litinin, 18 ga Nuwamba.

Advertisement

Kamfanin Dilancin Labarai ta Naija News Hausa ta fahimci cewa hukumar INEC ta a jagorancin Farfesa Orunmuwese ta mayar da dan takarar APC a matsayin wanda ya lashe zaben Bayelsa da ya fito takara bayan da ya sami mafi yawan kuri’u a zaben.

Advertisement
Advertisement

Rahoton ya bayyana Lyon da samun yawar kuri’u 352,552 da ya kaishi ga kayar da abokan karawarsa da kuma dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), babbar jam’iyyar adawa ta Najeriya, Duoye Diri, wanda ya sami yawar kuri’u 143,172.

Advertisement
Advertisement

Wannan sakamakon zaben da rahoton nasarar David Lyon ya tabbatar da jihar Bayelsa a zaman jihar APC, musanman sake lashe zaben Jihar a wannan karo kuma.

Advertisement