Connect with us

Uncategorized

Kogi: Ga Sakamakon Runfunan Zabe Da INEC ta Gabatar a Jihar Kogi a Yanzu

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

A yayin da ‘yan Asalin Kogi da ‘yan Najeriya ke duba da cike da tsammani, kwamishinan hukumar zaben jihar Kogi, Farfesa James Apam a halin yanzu yana karbar sakamakon ne daga kananan hukumomi shida.

Naija News ta fahimci cewa, Hukumar Zaben, INEC ta fara kirgan sakamakon zaben ne tsakankanin hukumomin tsaro, motocin sintiri da aka tura a kusa da ofishin INEC da cibiyar tattara sakamakon zabe a Lokoja.

Farfesa James Apam, kwamishinan zaben jihar Kogi ya gabatar ne d cewa a halin yanzu an samu sakamako ne daga kananan hukumomi shida don bayyanawa.

A yayin da masu sa ido, manyan shugabannin INEC suka yi zaman dirshan a cikin zauren Mahmood Yakubu inda sanarwar za ta gudana, an hana ‘yan jaridar da yawa shiga zauren. Jami’an INEC sun ce hana damar shiga aikin ‘yan jarida ya zama dole saboda rashin isheshen fili a cikin zauren.

Ka tuna da cewa hadi da sakamakon zaben ya kunshi zabe ta karo biyu ga kujerar Sanata a gundumar Kogi ta yamma.

Karanta Sakamakon Zaben Kananan Hukumomi da aka bayar a kasa;

Karamar Hukumar Ogori/Magongo

APC 3,679

PDP 2,145

SDP 244

Ijumu LG

APC 11,425

PDP 7,587

SDP 223

Karamar Hukumar Omala

APC 8,473

PDP 114,403

SDP 567

Karamar Hukumar Adavi

APC 64,657

PDP 366

SDP 279

Karamar Hukumar Igalamela/Idolu
APC 8,075
PDP 11,195
SDP 208

Karamar Hukumar Okene
APC 112,764
PDP 139
SDP 50

Karamar Hukumar Kabba/Bunu
APC 15,364
PDP 8,084
SDP 364

Karamar Hukumar Koton Karfi
APC 14,097
PDP 9,404
SDP 657