Connect with us

Uncategorized

Kogi: Karya Ne ba a bi na Bashin Albashin Ma’aikata – Yahaya Bello

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Gwamna Jihar Kogi, Yahaya Bello ya karyata rahoton da ke cewa ana bin sa bashin albashin ma’aikata a Jihar, ya lura cewa irin wannan rahoton karya ne.

Gwamnan jihar Kogi ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta gamu da alawus din ma’aikatan da ke jihar kuma ya nace cewa gwamnatinsa ba ta bin ma’aikata bashin ko taro.

Bello yayin da yake magana a gidan talabijin na Channels TV ya zargi ‘yan ta’addan jam’iyyar Peoples Democratic Party da soke wani mazaunin shiyarsu bayan da aka ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben Nuwamba 16.

Zababben gwamnan na jihar Kogi ya yi zargin cewa har ma da matar mataimakinsa an harbe ta bayan da ya lashe zaben gwamnan.

“Duk wadannan rahotannin da ni ke samu na albashi karya ne. Gwamnonin da suka gabata a Jihar Kogi sun mallaki albashin ma’aikata, tun daga wa’addin Audu zuwa magabaci na. Jihar Kogi ba ta bin kowa bashi a kowane sashi, abin da ya rage kawai shi ne kashi goma daga gwamnatin da ta gabata.” inji Yahaya Bello.

“Game da durkusawar El-Rufai, yana rokon mutanen jihar ne su yiwa Bello afuwa don tabbatar da cewa cika da tsaro, zaman lafiya, ba wai saboda ya kasa biyan albashi ba.”