Connect with us

Labaran Najeriya

Buhari Ya Shugabanci Taron FEC na farko bayan Dawowa daga Kasar London

Published

on

Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari a yau Laraba, 20 ga watan Nuwamba ya jagorancin taron Majalisar zartarwa ta tarayya wanda ya kasance taron farko bayan dawowar sa daga kasar Landan.

Naija News Hausa ta fahimci cewa taron da ake yi a birnin Tarayya, Abuja, itace zaman shugaban na farko bayan dawowa daga ziyarar da shugaban ya kai a Burtaniya.

Ka tuna da cewa mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ne ke jagorantar taron na FEC a lokacin da Buhari ya ke a can burtaniya a ziyarar kwanaki 15 da ya tafi.

Rahoto ya bayyana da cewa Osinbajo tare da wasu ministocn kasar da dama sun halarci a taron da ake a yau.

Kamin aka kafa kai ga taron, anyi juyayi na ‘yan mintuna don girmama tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Marigayi Mista Ufot Ekaette, da wani tsohon Ministan Yada Labarai, Marigayi Cif Alex Akinyele.


Get New DJ Mixes

KARANTA WANNAN KUMA; Ba na Tsoron Mutuwa – inji Tsohon Shugaban ƙasa Obasanjo