Connect with us

Labaran Najeriya

Buhari Ya Shugabanci Taron FEC na farko bayan Dawowa daga Kasar London

Published

on

at

Advertisement

Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari a yau Laraba, 20 ga watan Nuwamba ya jagorancin taron Majalisar zartarwa ta tarayya wanda ya kasance taron farko bayan dawowar sa daga kasar Landan.

Advertisement
Advertisement

Naija News Hausa ta fahimci cewa taron da ake yi a birnin Tarayya, Abuja, itace zaman shugaban na farko bayan dawowa daga ziyarar da shugaban ya kai a Burtaniya.

Advertisement

Ka tuna da cewa mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ne ke jagorantar taron na FEC a lokacin da Buhari ya ke a can burtaniya a ziyarar kwanaki 15 da ya tafi.

Advertisement
Advertisement

Rahoto ya bayyana da cewa Osinbajo tare da wasu ministocn kasar da dama sun halarci a taron da ake a yau.

Advertisement

Kamin aka kafa kai ga taron, anyi juyayi na ‘yan mintuna don girmama tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Marigayi Mista Ufot Ekaette, da wani tsohon Ministan Yada Labarai, Marigayi Cif Alex Akinyele.

Advertisement
Advertisement

KARANTA WANNAN KUMA; Ba na Tsoron Mutuwa – inji Tsohon Shugaban ƙasa Obasanjo

Advertisement
Advertisement