Connect with us

Labaran Najeriya

Shugaba Buhari Na Ganawar Siri da Majalisar Zartarwa

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministocin kasar suna halartar taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako da mako a Abuja.

Naija News ta gane da cewa Taron na gudana ne a zauren majalisa na fadar Shugaban kasa.

Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Mista Boss Mustapha suma sun halarci taron.

An bayyana da cewa taron sirin ya fara ne jim kadan bayan bude taro da addu’a daga bakin Ministan ayyuka da gidaje, Mista Babatunde Fashola, da Ministan Harkokin Wajen, Mista Geoffrey Onyeama.

A cikin wata sanarwa da Naija News Hausa ta ruwaito a baya, Shugaba Muhammadu Buhari ya gargadi shugabancin jam’iyyar All Progressive Congress (APC) kan tabbatar da cewa Jam’iyyar ba ta rusheba bayan ya karshe wa’adinsa a shekarar 2023.

Da shugaban yake jawabi a wurin taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) na jam’iyyar a Abuja, ranar Juma’a, ya kara da cewa Jam’iyyar za ta zama tarihi ne kawai idan har ta iya kasancewa da karfi kuma tana da matukar kulawa da talakawa.