Connect with us

Uncategorized

Kogi: Yahaya Bello Ya Bada Umarnin Korar Manyan Ma’aikata A Karkashinsa

Published

on

at

Advertisement

Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya umarci duk masu rike da mukaman siyasa su mikar da matsayinsu ga mafi girman ma’aikatan farar hula a ma’aikatar su, sashen su da kuma hukumar (MDA).

Advertisement
Advertisement

Sanarwar wacce aka rattaba hannu da kuma bayar a ranar Litinin ta hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Dakta Folashade Arike Ayoade ta lura cewa an raba wadannan a kasa da matsayinsu a yanzu.

Advertisement

“Dukkanin kwamishinoni, Darakta-Janar a harabar shugabancin Gidan Gwamnatin jihar. Ma’aikata ga Gwamna, Ma’aikata ga Mataimakin Gwamna, Ma’aikata ga shugaban Ma’aikata, Ma’aikata ga Mai Martaba, matar gwamnan da kuma mataimakiyarta, Matar Mataimakin Gwamna.”

Advertisement
Advertisement

Sanarwar ta ci gaba da bayyana cewa umarnin bai shafi “Shugaban Ma’aikatar Babban Sakatare-Janar na jihohi da Karamar Hukumar, Ciyamomi da Membobin kwamitocin jihar ba.”

Advertisement

“Dole ne a kawo karshen mikawar matsayin a ranar Talata, 3 ga Disamba, 2019. A mikar da kwafin bayanai na barin matsayin ga ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Kogi a kwafi mai laushi da kuma a takarda”

Advertisement
Advertisement

Sanarwar ta kara da cewa, “Sabuwar Dokar Gwamnatin Jihar ta nuna godiya ga jami’an da abin ya shafa don irin gudummawar da suka bayar wajen ci gaban jihar a wa’adin nasu.”

Advertisement
Advertisement