Connect with us

Uncategorized

Mahara Da Bindiga Sun Sace ‘Yan Sanda Biyu A Jihar Adamawa

Published

on

at

Advertisement

Alhaji Ahmadu Dahiru, Shugaban Hukumar Kula da Canji, karamar hukumar Mubi ta kudu a Adamawa, ranar Asabar ya ce wadanda ake zargi sun sace wasu ‘yan sanda biyu sun kuma sace mutane bakwai a karkarar.

Advertisement
Advertisement

Bisa hirar Dahiru da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a Gyela, ya ce; lamarin ya faru ne a kan hanyar Mubi zuwa Gyela, a ranar Talatar da ta gabata.

Advertisement

“Masu satar mutane suna tsoratar da kuma tsananta wa al’ummominmu a kullayomi, suna satar mutane da gangan a dare da rana. Sun kashe jami’an tsaro biyu a ranar Talatar da ta gabata wadanda suka yi sintiri a kan hanyar Mubi da Gyela.”

Advertisement
Advertisement

“A haka da nike magana da ku, kwanaki uku da suka gabata sun sace mutane biyar a Kwaja da biyu kuma a ?auyen Sauda,” in ji Dahiru.”

Advertisement

Ya bayyana da cewa, barayin sun yi ta tururuwa ne a saman wasu tsaunuka kusa a iyakar Najeriya da Kamaru.

Advertisement

Dahiru ya kara da cewa, al’ummomin sun yi asarar miliyoyin nairori ga masu garkuwa a yayin neman kubutar da wadanda aka sace daga hannunsu.

Advertisement
Advertisement

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Adamawa, DSP Sulaiman Nguruje ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an tura wata rundunar jami’an tsaro don magance matsalar a yankin.

Advertisement
Advertisement

Ya kuwa yi kira ga jama’ar jihar da su kai rahoton duk wani alamun hari ko shigar ‘yan garkuwa da suka gane da shi zuwa ofishin tsaro mafi kusa.

Advertisement