Connect with us

Uncategorized

FRSC: Hadarin Mota Ya Kashe Mutane 12 a Neja

Published

on

at

Advertisement

Hukumar kiyaye haddura ta tarayya (FRSC), a jihar Neja ta bayyana cewa mutane 12 ne suka mutu a wani hadarin mota da ya faru a ranar Lahadi a kauyen Sawmill da ke kan hanyar Mokwa zuwa Makera, a karamar hukumar Mokwa ta jihar.

Advertisement
Advertisement

Kwamandan Rundunar FRSC a yankin jihar, Mista Joel Dagwa, ya fada wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ranar Litinin a Minna cewa hatsarin ya faru ne da wata motar da ke dauke da rajista mai lamba KJ 555 XX, akan hanyarta zuwa Legas.

Advertisement

Dagwa a cikin bayaninsa ya ce motar da ta zo daga Maiduguri, ta dauki fasinjoji ne daga Zariya a cikin jihar Kaduna kafin ta nufi birnin Legas.

Advertisement
Advertisement

“Hadarin ya shafi mutane 103; Mata 55, maza 40, 8 yara. 12 daga cikinsu sun mutu yayin da 91 suka samu raunuka amma dai an kai su babban asibiti na Mokwa don yi musu magani.”

Advertisement

Ya kuwa danganta hadarin motar da yawar gudu daga hannun direban motar.

Advertisement

Kwamandan sashen yayi jaddada cewa rundunar za ta ci gaba da sa ido kan matafiya akan hanyar don kiyaye yawar lodi da tuki mai hadari.

Advertisement
Advertisement
Advertisement

“Tun daga wannan lokacin mun fara zirga-zirgar yawon bincike da kula da tafiye-tafiye a dukkan manyan hanyoyin domin tabbatar da cewa masu amfani da titin sun bi ka’idodin zirga-zirgar ababen hawa da kiyaye ka’idodin titi kafin, lokacin bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara.” in ji shi.

Advertisement