Connect with us

Labaran Najeriya

Muna Zantawa Da Buhari Kan Yanayin El-Zakzaky – Gwamnatin Iran

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Iran Ta Tattaunawa Da shugaba Buhari Kan Zancen El-Zakzaky

Gwamnatin Iran ta sanar da cewa tana cikin tattaunawa da Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya kan batun jagoran Harkar Musulunci a Najeriya, IMN, da aka fi sani da ‘Yan shi’a, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky.

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Abbas Mousavi, ya ce kasar tasu ta hanyar diflomasiya, tana hulda da gwamnatin Najeriya kan yanayin halin da El-Zakzaky ke a ciki.

Mousavi a hirar ya fadawa manema labarai a Tehran, babban birnin Iran a ranar Lahadin da ta gabata cewa Shugaba Buhari da Mataimakin Shugaban Harkokin tattalin arzikin Iran, Mohammad Nahavandian, sun gana kwanan nan a Malabo, Equatorial Guinea, kuma sun tattauna kan batutuwa da dama, ciki har da batun El-Zakzaky.

Taron ya gudana ne a yayin taron kolin kungiyar kasashen waje na fitar da Gas (GECF) a Equatorial Guinea.

Jami’in ya kara da cewa “Muna fatan cewa shawarwari da shirye-shiryen da ake yi tare da gwamnatin Najeriya za su yi cinma buri a gagauci wajen warware wannan matsalar ta El-Zakzaky,” in ji jami’in na Iran.

Naija News ta tuna cewa El-Zakzaky yana a tsare tun Disambar 2015, bayan shi da magoya bayan sa suka yi artabu da sojojin Najeriya a cikin jerin gwanon Hafsan Rundunar Sojojin kasar, Tukur Buratai, a cikin Zariya a jihar Kaduna.

Bayan haka, hukumar DSS a ranar Jumma’a da ta gabata ta dauki El-Zakzaky da matarsa ​​Zeenat daga Ma’aikatarta zuwa Gidan Horon Al’umma da ke a Kaduna, kamar yadda Babban Kotun Jihar Kaduna ta umarce su da yi.