Connect with us

Uncategorized

‘Yan Bindiga sun Kashe Mutane Hudu a Yayin Kallon Gasar Wasan Kwallon Kafa a Kaduna

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

A wani rahoto da jaridar Daily Trust ta fitar, wacce Naija News Hausa ta samu a sanarwa, ta ce wasu mutane dauke da makamai sun harbe mutane hudu tare da raunata wasu hudu a wani hari a filin wasan kwallon kafa a kauyen Zunuruk na karamar hukumar Kaura a jihar Kaduna.

Rahoton ya bayyana da cewa Maharan sun kai hari ne a ranar Lahadin da ta wuce da yamma yayin da matasa suke kallon wata gasar kwallon kafa.

Wani shaida, wanda ya bukaci kada a sanar da sunansa ya ce maharan sun fito ne daga cikin wani daji da ke kusa da wajen, inda suka yi harbe harben bindigasu har da ya kai ga kashin mutane hudu a take.

Mai shaidar ya ce ci wannan lamarin ne ya kawo karshen wasan kwallon kafar yayin da masu kallo duka suka gudu don tsira da rayukansu.

Ya kara a cikin bayaninsa da cewa a wani kauyen Tsonje da ke kusa da shiyar, a safiyar ranar Lahadi din a yayin da mutanen garin suka farka da safiya sun gano gawar wani daga cikin mazaunin yankin da ya mutu sakamakon harbe-harben.

Ya ce wanda aka kashe din, mai suna Dogara Kazzah ya fita ne da dare a misalin karfe takwas na dare don yin fitsari a bakin daji a daren, amma bain takaici ba a ga dawowarsa ba, kawai ne an iske gawar jikinsa da safiyar sakamakon harbin bindiga a kashegarin Lahadi.

A lokacin da Aminiya ta ziyarci Asibitin Kafanchan da misalin karfe 10:30 na dare, an ga motar asibiti tana dauke da mutane uku daga cikin wadanda suka jikkata zuwa Kaduna bayan samun taimako na farko.